Manyan Labarai
Kaso 40 na matasa ne idan na samu dama – Atiku

Dan takarar shugabancin ƙasa na Jam’iyyar PDP a zaben 2023, kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bawa matasan Najeriya tabbacin barin kyakkyawan tarihi a gare su, idan aka bashi damar jagorantar al’ummar kasar.
Mataimaki na Musamman ga Atiku Abubakar kan kafafen yada labarai, Abdulrasheed Shehu, ya sanya wa hannu, ya ce, Atiku Abubakar ya bada wannan tabbaci ne a ranar Laraba 3 ga watan Agusta, lokacin da ya karbi bakuncin tawagar shugabannin PDP sabon karni, karkashin jagorancin babban daraktan ta Audu Mahmud a gidan sa dake Abuja.
Atiku ya sake jaddada aniyar sa, kamar yadda ta ke kunshe cikin kundin manufofin sa, na bawa matasa dama a gwamnatin sa ta hanyar ware musu kaso 40, inda kuma ya ce, zai yi sauye-sauyen da suka kamata, domin bada dama ga mata da matasa.
Wazirin Adamawa ya kara da cewa, a gwamnatin PDP ne kawai aka aiwatar da tsarin nan na kebewa mata kaso 35, inda ya ce, APC ba ta taba girmama wannan yarjejeniya ba.
Ya kuma koka game da halin da matasa suka sami kansu, inda ya yi alkawarin daidaita al’amuran. A saboda haka, ya ce, ilimi zai zamo babban ginshikin gwamnatin sa, domin bunkasa rayuwar matasa da habaka dimukuradiyya. Ya bayyana takaici kan yadda APC ta wargaza tsarin da gwamnatin PDP ta shimfida a baya.
Yayin da yake tabbatar da muhimmancin matasa Wajen Gina kasa, Dan Takarar na PDP ya jaddada cewar, zai yi aiki da bukatun zamani, tare da gudanar da gwamnati mai tafiya tare da kowa mai la’akari da banbance-banbancen dake tsakanin mu.
A nasa jawabin, jagoran ayarin, Audu Mahmud ya ce, Atiku Abubakar wata mabubbuga ce, ta karfafa gwiwa da kyakkyawan tunani ga matasan kasar nan, inda ya bayyana yakinin da yake da shi na kwarewar Atiku domin magance matsalolin tattalin arziki da matsalolin siyasa domin amfanin dukkan yan Najeriya.

Manyan Labarai
Babu ɗaga Ƙafa tsakanin mu da Ƴan Daba da masu ƙwacen Waya a Kano – Anty Snaching Phone

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Wayoyin jama’a da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye ta Anty Snaching Phone, ta gargaɗi matasan da suke addabar al’umma da faɗan Daba a cikin birnin jihar Kano, da su ƙauracewa hakan domin ba za su saurarawa dukkanin wanda ya faɗa komar su ba.
Kwamandan rundunar tsaron a jihar Kano Inuwa Salisu Sharaɗa, shi ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, ya ce duk wanda suka kama da laifi musamman ma na faɗan Daba, ko ƙwacen waya ko kuma sha da dillancin kayan maye, za a ɗauki tsattsauran mataki akan sa.
“Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu ƙwacen Wayoyin jama’a, da Faɗan Daba, da kuma masu Sha da dallancin kayan Maye a jihar Kano, kuma duk wanda mu ka kama sai mun miƙa shi gurin da ya dace don ɗaukar Mataki, “in ji Inuwa Sharaɗa”.
Ya kuma buƙaci iyaye da su ƙara sanya idanu wajen kula akan shige da ficen ƴaƴan su, ta yadda za su zama ababen koyi a tsakanin al’umma.
Manyan Labarai
Za’a hukunta duk ma’aikacin Shari’ar da aka samu da laifi – Babbar Jojin Kano

Babbar jojin Kano mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jaddada cewar kwamitin ladabtarwa na hukumar Shari’a a jihar, zai hukunta duk wani ma’aikaci a tsagin Shari’a matuƙar aka same shi da laifin cin-hanci da rashawa.
Mai Shari’a Dije Aboki ta bayyana hakan ne a yayin taron ƙarawa juna sani wanda hukumar shari’ar ta gudanar ranar Talata, a ɗakin taro na Murtala Muhammad Library da ke Kano.
Taron an shirya shi ne don tunasar da sabbin ma’aikatan Shari’a, akan nauyin da ya hau kan su don mayar da hankali sosai akan batun gujewa cin-hanci da rashawa.
Babbar mai Shari’ar Dije Abdu Aboki, ta bayyana cewar akwai takaddu masu ɗauke da lambobin wayarta da aka liƙe a bangon kotuna, kuma duk wanda aka yi wa ba dai-dai ba zai iya sanar da ita ta kan lambobin kuma za a dauki mataki akan duk ma’aikacin da aka samu da laifi.
Wakilin tashar Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, a yayin taron taron ma’aikatan Shari’a da al’umma da dama ne suka samu damar halarta.
Hangen Dala
Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.
Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.
Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.
Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.
Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.
Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.
Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.
-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su