Siyasa
Ina tausayin talakawan Najeriya saboda yaudarar da ‘yan siyasa ke yi mu su – Wike

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya zargi wasu ‘yan siyasa a kasar da yin alkawuran karya, inda ya ce yana tausayin talakawan Najeriya da ke taso wa a nan gaba.
Gwamna Wike ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a wajen kaddamar da gadar sama da kasa ta Ikoku da Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a jihar Ribas ya yi.
A cewarsa: “Wani abin da ke damun kasar nan shi ne, wasu daga cikinmu, mu duka, ina tausaya wa talakawan Najeriya, ina tausaya musu, wasu na zuwa su fada mani, su goyi bayan wannan mutum, sai na ce, kun san shi?
“Abin da na ji shi ne mutane suna zuwa taron gari kuma suna nuna kowane irin abubuwan da suke faɗa. Sun ce za su aiwatar da gyaran fuska, za su tabbatar da cewa kowace shiyya za ta samu memba a majalisar tsaro, cewa ba shi da kyau shiyya daya ta mallaki dukkan shugabannin tsaro.
“Ka ga, amma yana da kyau yanki daya ya mamaye dukkan mukaman jam’iyya. Ka ga yadda ‘yan Nijeriya suke. Dubi yadda muke. Zan aiwatar da cewa kowace shiyya za ta wakilce ni, zan aiwatar…wato muhawarar da ake yi a talabijin domin kowa yana son ’yan Najeriya su ce eh, amma babu wani dan Najeriya da zai ce ‘mu fara daga jam’iyya.

Siyasa
Rurum ya sanar da ficewa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC a zauren Majalisar Wakilai

Shugaban majalisar Wakilai ta Ƙasa Tajudden Abbas, ya karanta takardar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Rano, Kibiya da Bunkure, RT. Honarable Kabiru Alhassan Rurum, ta ficewarsa daga Jam’iyyar NNPP zuwa Jam’iyyar APC, a hukumance.
Tajuddeen Abbas, ya karanta takardar sauyin sheƙar da Rurum din yayi a harabar Majalisar, a zamanta na yau Alhamis.
Wannan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da mai bai wa Rurum, shawara na musamman akan shafukan sada zumunta Fatihu Yusuf Bichi, ya fitar a ranar Alhamis 15-05-2025.
Tun dai a baya an jiyo yadda Honarable Kabiru Alhassan Rurum, ya sanar da ficewar sa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC, wanda a yanzu na tabbatar da ficewar tasa a hukumance a zauren Majalisar Wakilai ta ƙasa.

Hangen Dala
Yau shugaban kasa zai dawo daga Faransa

Bayan ziyarar aiki ta kusan mako biyu Zuwa kasar Faransa a yau litinin ake saka ran shugaban kasa zai dawo gida Nigeria.
Cikin sanarwar da hadimin shugaban kasar kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar ya ce kowa ne lokaci daga yanzu shugaban kasa Asuwaju Bola Tinubu zai sauka a Nigeria domin cigaban da harkokin mulkin kasar.

Hangen Dala
Kofar APC a bude take ga masu shiga – Abdullahi Abbas

Jamiyyar APC a Jihar Kano tace Kofar ta a bude take ga dukkanin masu son shigowa jamiyyar.
Shugaban jamiyyar na Kano Hon Abdullahi Abbas ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai.
Abbas yace labarin dake yawo cewa akwai wadanda ke Shirin shigowa jamiyyar, su sani Kofar APCn a bude take tare da maraba ga dukkanin wadanda zasu shigo.
Koda dai Abdullahi Abbas yace shigowa APC ba zai hana tuhuma kan zargin cin hanci da rashawa ba, koma kaucewa hukumar EFCC da ICPC.
A baya bayan nan ne dai aka rinka yada cewa mabiya jamiyyar NNPP kwankwasiyya na Shirin shiga jamiyyar APC tare da madugun ta Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su