Siyasa
Mun ƙudiri aniyar gyara tarbiyyar Matasa a jahar mu – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano tasha alwashin ci gaba da magance matsalar tsaro musamman wajen kawo karshen kwacen waya da harkar Daba da ake fama dashi a jihar kano.
Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ne ya bayyana hakan a yayin karɓar baƙuncin mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero, a fadar fadar gwamnatin Kano, a wani ɓangare na bikin hawan Nassarawa, da ya gudana a yau Juma’a.
Abba Kabir, ya kuma ce duk da matsalolin da gwamnatin Kano ta fuskanta a baya na harkar shari’a, amma hakan bai hana ta cika alkawarin da ta ɗauka ga al’ummar jihar kano a yakin neman zaben shekarar 2023 da ta gabata ba.
Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ba ta tsaya ba sai da ta yi kokarin magance matsalar da harkar Ilimi ke fama dashi wajen gyara makarantu da fitar da ɗalibai kasahen waje dan karo Ilimi kyauta.
“Gwamnatin mu ta bijiro da tsarin tallafawa masu harkar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da harkar Daba, da sana’oin dogaro da kai domin kawo karshen Daba a jihar kano, “in ji Gwamna Abba Kabir”.
Hawan Nasarawa dai hawa ne da ake sada zumunci a tsakanin masarautar Kano da gwamnatin Jihar Kano, da kuma al’ummar jihar, wanda da aka saba gudanar da shi a duk rana ta uku, na bikin ƙaramar Sallah, da Babba.
Da yake jawabi tunda farko mai martaba sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yabawa gwamnatin Kano akan tsarin da ta fito dashi na ciyar da al’ummar jihar kano gaba, musamman ma tsarin ciyarwar azumi da tayi ga mabukata a watan Ramadan da ya gabata.
Ya ci gaba da cewa, “Wannan ciyarwar ga al’umma tsari ne da ya kamata ya ɗore domin rage raɗaɗi da yunwa da ake fama da ita; muna shawartar Gwamnatin Kano, da ta saka ido sosai wajen kawo ƙarshen Daba da ƙwacen waya da hawa doki ana sukuwa ba bisa ka’ida ba, “in ji Sarkin”.
Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito mana cewa, Sarkin ya kumashawarci gwamnatin Kano, da ta ƙara dagewa wajen ci gaba da tallafawa Ilimin ɗalibai da ke fadin jihar kano, da sauran ayyuka da za su kawo wa jihar kano ci gaba.

Baba Suda
Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.
Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.
Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Labarai
Tsohon shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan ya ƙaryata ficewar sa daga APC zuwa SDP

Tsohon shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan, ya musanta wata jita-jita da ake yaɗawa kan cewar ya fice daga cikin jam’iyyar APC mai mulki a ƙasa, zuwa SDP, al’amarin da ya ce bashi da tushe ballantana makama.
A cikin wata sanarwar da mashawarci na musamman ga tsohon Sanatan a kafafen yaɗa labarai Ezrel Tabiowo, ya fitar a jiya Lahadi, ta ce jita-jitar da ake yaɗawa na cewar Ahmad Lawan ya fice daga jam’iyyar ta APC, ƙarya ce tsagwaronta.
Jaridar Daily trust ta ruwaito cewar, sanarwar ta kuma ce, har yanzu Ahmad Lawan ɗan Jam’iyyar APC ne, kuma yana biyayya ga jam’iyyar, wadda yake alfahari da ita.

Hangen Dala
Lauyoyin gwamnatin Kano sun bukaci a kamo Ganduje

Babbar kotun jaha mai lamba 7 karkashin jagorancin mai sharia Amina Adamu ta sanya karfe biyu da rabi na ranar yau dan bayyana matsayarta akan batun gurfanar da tsohon gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa da wasu mutane.
A zaman kotun na yau lauyoyin gwamnatin jaha sun bayyana wa kotun cewa an sadar da sammace ga wadanda ake kara ta hanyar kafafen yada labarai kamar yadda kotun ta yi umarni tun a baya amma wadanda ake kara basu samu damar halartar kotun ba dan haka ya roki ko dai a kamo su ko kuma kotun ta ci gaba duk da cewar basa gaban kotun.
Sai dai lauyan wanda ake kara na 6 barrister Nuraini Jimo SAN ya yi suka inda ya bayyana cewar kotun ta dakata tun da sun daukaka kara ya kuma bayyana cewar kotun bata da hurumi sannan kunshin tuhume-tuhumen yana dauke ta kura-kurai.
Kotun zata bayyana matsayarta a yau da rana.
Tun da farko gwamnatin kano ta yi karar Ganduje da mutane 6 bisa zargin almundahana akan kudi sama da Naira Biliyan 4 da aka yi zargin sun sayarda wasu filaye sun raba kudin.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su