Connect with us

Siyasa

Mun ƙudiri aniyar gyara tarbiyyar Matasa a jahar mu – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin Kano tasha alwashin ci gaba da magance matsalar tsaro musamman wajen kawo karshen kwacen waya da harkar Daba da ake fama dashi a jihar kano.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ne ya bayyana hakan a yayin karɓar baƙuncin mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero, a fadar fadar gwamnatin Kano, a wani ɓangare na bikin hawan Nassarawa, da ya gudana a yau Juma’a.

Abba Kabir, ya kuma ce duk da matsalolin da gwamnatin Kano ta fuskanta a baya na harkar shari’a, amma hakan bai hana ta cika alkawarin da ta ɗauka ga al’ummar jihar kano a yakin neman zaben shekarar 2023 da ta gabata ba.

Ya ƙara da cewa gwamnatinsa ba ta tsaya ba sai da ta yi kokarin magance matsalar da harkar Ilimi ke fama dashi wajen gyara makarantu da fitar da ɗalibai kasahen waje dan karo Ilimi kyauta.

“Gwamnatin mu ta bijiro da tsarin tallafawa masu harkar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da harkar Daba, da sana’oin dogaro da kai domin kawo karshen Daba a jihar kano, “in ji Gwamna Abba Kabir”.

Hawan Nasarawa dai hawa ne da ake sada zumunci a tsakanin masarautar Kano da gwamnatin Jihar Kano, da kuma al’ummar jihar, wanda da aka saba gudanar da shi a duk rana ta uku, na bikin ƙaramar Sallah, da Babba.

Da yake jawabi tunda farko mai martaba sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yabawa gwamnatin Kano akan tsarin da ta fito dashi na ciyar da al’ummar jihar kano gaba, musamman ma tsarin ciyarwar azumi da tayi ga mabukata a watan Ramadan da ya gabata.

Ya ci gaba da cewa, “Wannan ciyarwar ga al’umma tsari ne da ya kamata ya ɗore domin rage raɗaɗi da yunwa da ake fama da ita; muna shawartar Gwamnatin Kano, da ta saka ido sosai wajen kawo ƙarshen Daba da ƙwacen waya da hawa doki ana sukuwa ba bisa ka’ida ba, “in ji Sarkin”.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito mana cewa, Sarkin ya kumashawarci gwamnatin Kano, da ta ƙara dagewa wajen ci gaba da tallafawa Ilimin ɗalibai da ke fadin jihar kano, da sauran ayyuka da za su kawo wa jihar kano ci gaba.

Hangen Dala

Take hakki:- Matakin Amnesty game da kama wasu ‘yan jarida a Kano

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Amnesty International, ta yi ala-wadai da cin zarafin ‘yan jarida biyu a Kano, wato mawallafin jaridar kano Times, Buhari Abba da kuma Isma’il Auwal.

Cikin sanarwar sa Ƙungiyar ta wallafa a shafin ta na facebook,
ta ce babu shakka abin da rundunar ‘Yansandan jihar Kano ta yi bisa umarnin Kwamishinan yaɗa labaran jihar, Ibrahim Waiya abin takaici ne.

Rundunar ‘Yansandan jihar Kano dai ta gayyaci Buhari Abba zuwa sashin binciken manyan laifuka (CID) ne, harma kuma ta tsare shi na tsawon awanni.

Kuma dai ana tuhumar mutanen biyun ne da zargin ɓata sunan kwamishinan, ta hanyar wani ra’ayi da jaridar ta wallafa wanda Isma’il Auwal ya rubuta.

Kungiyar ta Amnesty ta ce duk ba zata lamunci duk wani yunƙuri na takewa waɗannan ‘Yan jarida haƙƙinsu ba.

A ƙarshe ƙungiyar taja hankalin gwamantin kano da kuma rundunar ‘Yansandan jihar, da su guji yunƙurin daƙile ‘yancin faɗin albarkacin baki.

Continue Reading

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Labarai

Tsohon shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan ya ƙaryata ficewar sa daga APC zuwa SDP

Published

on

Tsohon shugaban majalisar Dattawa Ahmad Lawan, ya musanta wata jita-jita da ake yaɗawa kan cewar ya fice daga cikin jam’iyyar APC mai mulki a ƙasa, zuwa SDP, al’amarin da ya ce bashi da tushe ballantana makama.

A cikin wata sanarwar da mashawarci na musamman ga tsohon Sanatan a kafafen yaɗa labarai Ezrel Tabiowo, ya fitar a jiya Lahadi, ta ce jita-jitar da ake yaɗawa na cewar Ahmad Lawan ya fice daga jam’iyyar ta APC, ƙarya ce tsagwaronta.

Jaridar Daily trust ta ruwaito cewar, sanarwar ta kuma ce, har yanzu Ahmad Lawan ɗan Jam’iyyar APC ne, kuma yana biyayya ga jam’iyyar, wadda yake alfahari da ita.

Continue Reading

Trending