Baba Suda
Shirin Baba Suda na ranar Alhamis 13/02/2020 tare da Aliyu Wali

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Baba Suda
Ƴan Nigeria miliyan 20 ne ke da taɓin-hankali – WHO

Wani rahoto da hukumar lafiya ta duniya, WHO, ta fitar ya ce ƴan Najeriya miliyan 20, daidai da kashi 20 cikin 100 na al’ummar kasar, na fama da matsalar taɓin-hankali.
Dr Azubike Aliche, Sakataren Kwamitin Amintattu na Cibiyar Kula da Lafiyar Ƙwaƙwalwa ta Najeriya-Amurka (NAIMH) ne ya bayyana haka a wani shirin horo kan lafiyar kwakwalwa da GAP Action da cibiyar su ka shirya a Owerri a jiya Talata.
Ya bayyana cewa “lamarin mai tayar da hankali ne” game da ciwon damuwa da ƴan Nijeriya ke fama da shi, wanda ya ce, ya kasance mafi girma a duniya kuma ya yi kira da a yi ƙoƙari matuƙa don canza yanayin.
“Rahotanni da ake samu sun nuna cewa kashi 10 cikin 100 na masu fama da tabin hankali ne kawai ke samun kulawa a Najeriya kuma dole ne a canza wannan yanayi,” in ji shi.
TRT Hausa

Baba Suda
Dumamar yanayi :- Gwamna Zulum ya haramta sare bishiyu

Gwamnan jihar Borno Baba Gana Umar Zulum ya kaddamar da wasu dokokin biyu ga al’ummar Jihar.
Dokar farko itace Gwamnan ya haramta sare bishiyu a dukkanin fadin jihar, Inda kuma ya Kara kaddamar da dokar tsaftace muhalli a dukkanin karshen wata.
Yayin da yake kaddamar da dokar Gwamna Zulum yace duba da dumamar yanayi da ake fuskanta a yanzu gwamnati ta haramta sare bishiyu a fadin jihar Borno.
Haka kuma saboda Kare lafiya da kuma al’ummar Jihar dole ne dukkanin karshen wata a gudanar da tsaftar muhalli a Jihar Borno.
” A matsayi na Wanda kundin tsarin mulkin kasa ya bani dama, ni Baba Gana Umara Zulum na haramta sare bishiyu a fadin jihar Borno, kuma na saka dokar wajibi ne kowa ne dan Jihar ya tsaftace muhalli a dukkanin karshen wata, saboda inganta lafiyar al’ummar Jihar Borno.”

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su