Connect with us

Labarai

Kai Jama’a: Uwa ta kona hannun ‘yar ta mai shekaru 5 saboda ta cinye mata Kifi na siyarwa

Published

on

An zargi wata mata mai ‘ya’ya biyu, Tina Idoroyen da sanya hannun ‘yarta ‘yar shekara biyar a cikin ruwan zafi saboda zargin ta sace mata  kifi.

Tina Idoroyen wacce ta ke a titin Gregory, unguwar Ikot Ansa a karamar hukumar Calabar ta jihar Cross River.

Matar  mai sayar da kifi ta ce, ta shirya kifi guda 19, domin sana’arta, sannan ta fita, amma sai kifi guda daya kawai ta tarar bayan ta dawo.

Ta gano cewa ’yarta mai shekara 5 ta cinye kifin, domin haka ta hukunta ta ta hanyar tsoma hannunta cikin ruwan zafi, in ji Guardian.

Counsel to Basic Rights Counsel Initiative (BRCI), kungiya ce masu zaman kansu, kuma wadda mai kula da sashin yara, Mista James Ibor, ya yi zargin cewa, mahaifiyar ta yarda cewa yarinyar ba ta ci abinci ba kafin ta ci kifin, wanda hakan ya nuna cewa da alama yunwa ta ke ji.

Ya ce: “Mahaifiyar ta yi zargin cewa, ‘yarta ‘yar shekara biyar ta sace kifin ta, domin haka ta tsoma hannunta a cikin wani ruwan zafi mai tsananin gaske, haka ta mayar da martani kan zargin satar.

“Matar ba ta da komai, mahaifin yaron ya yi watsi da su shekaru biyu da suka wuce, kuma har yanzu ta na da wata ‘yar shekara takwas. 

Mista Ibor ya ce ba a kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda ba, saboda yarinyar na bukatar tallafi da kulawar mahaifiyarta yayin da ta ke asibiti ta na jinya.

Ibor, wanda ya bayar da tabbacin cewa nan ba da dadewa ba za a mika wanda ta aikata laifin ga ‘yan sanda, domin gurfanar da ita, ya kuma bayyana cewa an dauke yarinyar daga wani asibiti mai zaman kansa zuwa babban asibitin Calabar, inda kwararru ke kula da lafiyarta.

Labarai

Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama

Published

on

Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.

Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.

Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.

Continue Reading

Labarai

Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam

Published

on

Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.

Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.

Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.

Continue Reading

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Trending