Connect with us

Labarai

APC RESHEN JIHAR KWARA BA ZA TA TABA JUYA WA BUKOLA SARAKI BAYA BA

Published

on

Jam’iyyar APC reshen jihar Kwara ta ce ba za ta taba juya wa shugaban majalisar Dattawa Sanata Bukola Saraki baya ba.

Shugaban jam’iyyar Ishola Fulani ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar inda yana mai nanata cikakken goyon bayan su ga sanata Saraki.

Mr Ishola Fulani a cikin sanarwar ya kara da cewa, shugabancin jam’iyyar APC a Kwara zai ci gaba da biyayya ga shugaban majalisar dattawan.

Kalaman shugaban APC na jihar Kwara na zuwa ne kasa da mako guda da kotun koli ta wanke Sanata Saraki daga tuhumarsa da aka yi masa game da yinkarya wajen bayyana kadarorinsa, kamar yadda dokokin kasa sukayi tanadi.

Gwamnatin tarayya ta jam’iyyar APC karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari ta gurfanar da sanata Bukola Saraki a gaban kotun da’ar ma’aikata tun a shekara ta 2015.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending