Connect with us

Manyan Labarai

AN BAYYANA RASHIN RIKO DA KOYARWAR MA’AIKI A MATSAYIN ABUN DA YA SABBABA LALACEWAR MATASA A WANNAN ZAMANI

Published

on

Wani malamin addinin musulinci a nan kano malam Musa Sidi Ibrahim, ya bayyana rashin riko da koyarwar ma’aiki S.A.W. a matsayin abun da ya sabbaba lalacewar matasa a wanan zamani.

Malam Musa Sidi ya bayyana hakanne, a wani taron maulidi daya gudana a unguwar Ajawa dake karamar hukumar gwale.

Ya kuma kara da cewa su matasa suna bukatar a jasu a jiki tare da dabbaka kyawawan halaye ta yadda zasu yi koyi.

A nasa jawabin jagoran gudanar da maulidin, malam Kabiru Abdussalam, y ace kamata ya yi malamai sun rinka gabatar da jawaban fadakar da al,umma kan halayen ma’aiki da suka zo cikin litattafan gabata, don ganin an dora su akan hanyar shiriya.

Wakilinmu Ibrahim Abdullahi Sorondinki ya rawaito cewa malamai da dama ne suka gabatar da jwabai a yayin taron maulidin.

Manyan Labarai

Dagatai da masu unguwanni ku guji ɓoye mana bayanan sirri akan ƴan Daba da masu fashin Waya – Rundunar Tsaro a Kano

Published

on

An buƙaci Dagatai da masu unguwanni da su guji ɓoye bayanan sirri akan ƴan Daba ko ɓata gari a duk lokacin da aka buƙaci sanin hakan dan ɗaukar mataki, domin gujewa abinda kaje ya dawo.

Mashawarci na musamman ga gwamnan Kano akan harkokin tsaro, kuma kwamandan rundunar tsaro masu rajin kawar da masu ƙwace wayoyi, da ɓata gari ta KOSSAP, Inuwa Salisu Sharaɗa, ne ya bayyana hakan ne a zantwar sa da gidan rediyon Dala FM Kano.

Ya kuma ce matuƙar dagatai da masu unguwannin za su rinƙa ɓoye musu bayanan sirrin a duk lokacin da suka ɓoƙaci sani, babu makawa hakan ka iya haifar da barazana ga rawanin su.

A cewar sa, “Mafi yawan lokuta idan muka je wajen masu unguwanni ko kuma dagatai, neman wani bayanan sirri akan wasu ɓata gari sukan ɓoye mana kuma ba zamu lamunci hakan ba zamu sanar da gwamna abinda ke faruwa, “in ji Inuwa Sharaɗa”

Inuwa Salisu, ya kuma ƙara da cewa a ƙoƙarin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, na magance matsalar tsaro a sassan jihar, ya samar da wani haɗakar jami’an tsaro wato Task Force, da za su rinƙa shiga lungu da saƙo, dan ganin tsaro ya inganta tare da kawar da masu fashi da makamin wayoyin mutane.

Inuwa, ya ci gaba da cewa, “Jami’an mu za su ci gaba da hoɓɓasa a ciki da wajen Kano wajen kawar da ɓata garin da suke addabar mutane a faɗin jahar mu; Duk wanda muka kama zai gayawa Aya zaƙin ta, “in ji shi”

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da neman ɗaukin mahukunta wajen magance matsalar tsaro a sassan jihar Kano, da ma ƙasa baki ɗaya.

Continue Reading

Manyan Labarai

Uku daga cikin mutane sama da 20 da wani matashi ya cinnawa Wuta cikin wani masallaci a Kano sun rasu

Published

on

Rahotanni da dumi-ɗumin sa na bayyana cewar yanzu haka uku daga cikin mutane sama da 20 da wani matashi ya cinnawa Wuta cikin wani masallaci a unguwar Larabar Abasawa da ke ƙaramar hukumar Gezawa a Kano sun rasu.

Wani mazaunin garin ya shaidawa Dala FM Kano, da tsakar ranar Larabar nan cewar, daga cikin mutane ukun da suka rasu har da limamin da ya jagorancin sallar asubar wannan rana, wanda a lokacin ne matashin ya cinna musu wutar lamarin da jikin su mutanen sama da 20 ya sassaɓule.

Idan dai ba’a manta ba matashin ya cinnawa mutanen wuta ne bayan da ya watsa Fetur cikin masallacin yayin da suke tsaka da sallar Asubah, ta wannan rana, wanda tuni jami’an tsaron ƴan sanda suka cika hannun su da shi.

Matashin dai ya ce ya cinnawa mutanen wutar ne biyo bayan wata magana da suke faɗa masa wanda ransa baya daɗi, ina ya sayo Fetur a cikin wani Galan lamarin da yaje ya kunna musu wutar, duk da shima hannayen sa biyu sun ƙone.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mun kama matashin da ya kunnawa mutane sama da 20 Wuta a cikin wani masallaci – Ƴan Sandan Kano

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta tabbatar da kama wani matashi da ake zargi da cinnawa wasu mutane Wuta, a lokacin da suke tsaka da Sallar Asubar yau Laraba, a cikin wani Masallaci a garin Larabawar Abasawa da ke ƙaramar hukumar Gezawa a Kano.

Kakakin rundunar ƴan sandan SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya aikowa Dala FM Kano, a yau Laraba, ya ce bayan samun rahoton faruwar al’amarin ne Kwamishinan ƴan sandan Kano CP Muhammad Usaini Gumel, ya tura tawagar jami’an su inda suka kai ɗaukin gaggawa.

Matashin da ake zargin mai suna Shari’u Abubakar ɗan shekaru shekaru 38, ya ce shine ya siyo Fetur ya kunna wutar inda ya wurgata a cikin masallacin, lamarin da ya sa mutane da dama suka ƙone a sassan jikin su.

“Aƙalla mutane 24 ne suka ƙone bayan da matashin ya kunna musu wutar a cikin masallacin, wanda tuni jami’an mu suka kai su asibitin Murtala Muhammad da ke Kano, inda suke ci gaba da samun kulawar likitoci, “in ji SP Kiyawa”.

Koyawa, ya kuma ce daga binciken farko da suka fara matashin ya tabbatar da cewa shine ya sayo Mai a gidan Mai a cikin wata roba, yazo ya kunna wutar, biyo bayan wani rikicin gado da a tsakanin sa da wasu daga cikin mutanen yankin su, inda shima hannayen sa biyu suka ƙone.

Continue Reading

Trending