Connect with us

Manyan Labarai

Daliban Najeriya dubu 15 za su shiga tsaka mai wuya bayan haramta digirin Benin – Kungiyar Dalibai

Published

on

Kungiyar daliban kasar nan ta bukaci gwamnatin Najeriya, da ta sake nazarta matakin haramta digirin Jamhuriyyar Benin, a cikin kasar lura da yadda hakan zai shafi akalla dalibai dubu 15 da yanzu haka ke tsaka da karatu a Coutonu.

Rahotanni sun bayyana cewa matakin haramta amfani da digirin ta Benin ya biyo rahoton yadda wani dan jarida ya yi basaja tare da kammala digirinsa cikin watanni 2 a kasar, tare da dawowa Najeriyar don fara bautar kasa, daga bisani ya saki abinda ya faru.

Akan kuma wannan dambarwar ne gwamnatin kasar ta haramta digirin daga makwabciyarta wato Coutonu, yayin da daga bisani ta fadada haramcin zuwa wasu kasashe da suka kunshi Uganda da Kenya da kuma Togo da Jamhuriyar Nijar, baya ga kasar Ghana.

Akan batun dakatarwar ne kuma shugaban kungiyar daliban Najeriya da ke karatu a Benin Ugochukwu Favour, yayin zantawarsa da gidan talabijin na Channels, ya roki gwamnatin kasar kan ta sake nazartar matakin tare da tantance ingancin jami’o’in gabanin zartas da makamancin hukuncin, kamar yadda kafar yada labarai ta RFI Hausa ta rawaito.

Ya ce akwai bukatar hukunta iya jami’ar da aka samu da tafka badakalar mai-makon yin kudin goro ga ilahirin jami’o’in da ke Benin din.

Ya kuma kara da cewar yanzu haka akwai daliban Najeriya fiye da dubu 15 da ke karatu a jami’o’I daban-daban da ke cikin kasar ta Benin, kuma daukar matakin kai tsaye zai wargaza rayuwarsu, musamman ma ta karatunsu.

Rahotanni sun yi nuni da cewar sai dai kuma ministan Ilimi na Najeriya, Tahir Mamman ya bayyana cewa, baya ko tausayawa daliban da ke karatu a kasashen da aka haramta, mai-makon haka ma kamata ya yi a tuhume su da aikata babban laifi.

Manyan Labarai

Zan saka hannu akan hukuncin da kotu za ta yanke wa wanda ya cinnawa masallata Wuta har 15 suka rasu – Gwamnan Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ya ce a shirye yake da ya saka hannu akan duk hukuncin da kotu zata yanke akan matashin da ake zargi da cinnawa masallata wuta a lokacin da da suke tsaka da sallar asuba cikin masallaci a kauyen Gadan dake karamar hukumar Gezawa a makon da mukayi bankwana dashi.

Injiniya Abba Kabir Yusif ya bayyana hakan ne a jiya Lahadi, yayin ziyarar gani da ido da ya kai Asibitin Murtala, inda majinyatan ke samun agajin likitoci, domin kula da su.

Gwamnan ya ce gwamnatin Kano na Allah wadai da wannan lamari, inda ya ce akwai tsantsar rashin imani a cikin sa ace mutane suna tsaka da Sallah azo a cinna musu wuta babu gaira babu dalili.

Rahotanni sun bayyana cewa aƙalla dai mutane goma sha biyar ne 15, ne suka rasa rayukansu sakamakon wannan iftila’in da ya afku a ranar Larabar da ta gabata, wanda ake zargi rabon gado ne sila.

Tuni dai rundunar ƴan sandan jihar Kano ta bakin Kakakin ta SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ta ce matashin mai suna Shafi’u Abubakar yana hannun ta ana faɗaɗa bincike, kuma da zarar an kammala za’a gurfanar da shi a gaban Kotu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Dagatai da masu unguwanni ku guji ɓoye mana bayanan sirri akan ƴan Daba da masu fashin Waya – Rundunar Tsaro a Kano

Published

on

An buƙaci Dagatai da masu unguwanni da su guji ɓoye bayanan sirri akan ƴan Daba ko ɓata gari a duk lokacin da aka buƙaci sanin hakan dan ɗaukar mataki, domin gujewa abinda kaje ya dawo.

Mashawarci na musamman ga gwamnan Kano akan harkokin tsaro, kuma kwamandan rundunar tsaro masu rajin kawar da masu ƙwace wayoyi, da ɓata gari ta KOSSAP, Inuwa Salisu Sharaɗa, ne ya bayyana hakan ne a zantwar sa da gidan rediyon Dala FM Kano.

Ya kuma ce matuƙar dagatai da masu unguwannin za su rinƙa ɓoye musu bayanan sirrin a duk lokacin da suka ɓoƙaci sani, babu makawa hakan ka iya haifar da barazana ga rawanin su.

A cewar sa, “Mafi yawan lokuta idan muka je wajen masu unguwanni ko kuma dagatai, neman wani bayanan sirri akan wasu ɓata gari sukan ɓoye mana kuma ba zamu lamunci hakan ba zamu sanar da gwamna abinda ke faruwa, “in ji Inuwa Sharaɗa”

Inuwa Salisu, ya kuma ƙara da cewa a ƙoƙarin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, na magance matsalar tsaro a sassan jihar, ya samar da wani haɗakar jami’an tsaro wato Task Force, da za su rinƙa shiga lungu da saƙo, dan ganin tsaro ya inganta tare da kawar da masu fashi da makamin wayoyin mutane.

Inuwa, ya ci gaba da cewa, “Jami’an mu za su ci gaba da hoɓɓasa a ciki da wajen Kano wajen kawar da ɓata garin da suke addabar mutane a faɗin jahar mu; Duk wanda muka kama zai gayawa Aya zaƙin ta, “in ji shi”

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da neman ɗaukin mahukunta wajen magance matsalar tsaro a sassan jihar Kano, da ma ƙasa baki ɗaya.

Continue Reading

Manyan Labarai

Uku daga cikin mutane sama da 20 da wani matashi ya cinnawa Wuta cikin wani masallaci a Kano sun rasu

Published

on

Rahotanni da dumi-ɗumin sa na bayyana cewar yanzu haka uku daga cikin mutane sama da 20 da wani matashi ya cinnawa Wuta cikin wani masallaci a unguwar Larabar Abasawa da ke ƙaramar hukumar Gezawa a Kano sun rasu.

Wani mazaunin garin ya shaidawa Dala FM Kano, da tsakar ranar Larabar nan cewar, daga cikin mutane ukun da suka rasu har da limamin da ya jagorancin sallar asubar wannan rana, wanda a lokacin ne matashin ya cinna musu wutar lamarin da jikin su mutanen sama da 20 ya sassaɓule.

Idan dai ba’a manta ba matashin ya cinnawa mutanen wuta ne bayan da ya watsa Fetur cikin masallacin yayin da suke tsaka da sallar Asubah, ta wannan rana, wanda tuni jami’an tsaron ƴan sanda suka cika hannun su da shi.

Matashin dai ya ce ya cinnawa mutanen wutar ne biyo bayan wata magana da suke faɗa masa wanda ransa baya daɗi, ina ya sayo Fetur a cikin wani Galan lamarin da yaje ya kunna musu wutar, duk da shima hannayen sa biyu sun ƙone.

Continue Reading

Trending