Connect with us

Manyan Labarai

Gwamnan Kano ya ƙaddamar da tallafin kayan abinci da gidauniniyar Dangote za ta rabawa mutane

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci ƙaddamar da rabon tallafin kayan abinci da gidauniniyar Dangote Foundation za ta rabawa al’ummar kasar nan, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa da suke fuskanta.

Da yake ƙaddamar da rabon tallafin a gidan gwamnati, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi kira ga kwamitin da za su gudanar da rabon kayan abincin su zamo masu gaskiya da rikon amana, tare da tabbatar da tallafin ya isa ga mabuƙatan da aka tanadi abincin domin su, su samu yadda ya dace.

Aƙalla dai mutane dubu dari da ashirin ne za su amfana da tallafin kayan abincin a jihar Kano (120), waɗanda suka hadar da masu kananan karfi, da kuma masu bukata ta musamman irin su masu larurar Ƙafa, da masu lalurar Ido, da sauransu.

Injiniya Abba Kabir Yusuf ya kuma ce tuni tallafin kayan abincin ya isa ga ƙananan hukumomin Kano 44.

“Mun gamsu bisa tsarin da gidauniyar ta Dangote tayi na shigar da dakarun hukumar Hisbah cikin tsarin rabon tallafin abincin, da kuma shuwagabannin ruko na kananan hukumomi 44, Muna fatan cewa za su tsaya kan adalci da gaski yayin gudanar da rabon kayan abincin, “in ji Gwamnan”.

Da yake gabatar da tallafin, Alhaji Aliko Dangote, ya ce mutane miliyan daya ne za su amafana da tallafin buhunan shinkafa da Gero, guda Goma-goma daga dukkanin jihohin kasar nan har da babban birnin tarayya Abuja.

Ɗangote, ya kuma kara da cewar Gidauniyar ta dauki gaɓarar tallafawa al’ummar kasar nan ne da kayan abinci tun lokacin da kasar nan ta tsintar kanta a cikin halin annobar cutar nan ta Covid 19, tun a shekarar 2019, har zuwa yanzu, inda ya ce gidauniyar ba a nan ta tsaya ba tana tallafawa a bangaren Lafiya da Ilimi.

Wakilinmu na fadar Gwamnatin kano Abba Haruna Idris ya rawaito cewa, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma godewa Alhaji Aliko Dangote, bisa samar da wannan tallafi, musamman a wannan yanayi na tsadar rayuwa da ake fuskanta tare da yin Kira ga mawadata da su yi koyi da irin wannan abin Alkhairi, domin samun gwaggwaɓan lada a wajen Ubangiji S.W.T. kamar yadda wakilinmu na fadar Gwamnatin Kano Abba Haruna Idris ya rawaito mana.

Manyan Labarai

Za’a ɗauki mataki akan duk wanda yake da hannu Gini ya ruftawa mutane a Kuntau – Ƙaramar hukumar Gwale.

Published

on

Yayin da wani ginin Bene mai hawa biyu ya danne aƙalla sama da Leburori goma a unguwar Kuntau kusa da KEDCO, a safiyar yau Juma’a, Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Gwale Abubakar Mu’azu Mojo, ya ce za’a ɗauki mataki akan dukkan wanda aka samu da laifi har al’amarin ya faru.

Abubakar Mu’azu Mojo, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da manema labarai, yayin da ya ziyarci gurin da lamarin ya faru lokacin da ake ci gaba da aikin ceto mutanen.

Mojo, ya kuma ce babu makawa za’a ɗauki matakin doka akan duk wanda aka samu da hannu akan faruwar lamarin, kama daga ɗan kwangilar da aka bai wa aikin ginin, zuwa kuma mamallakin gidan.

Rahotanni sun bayyana cewa zuwa tsakar ranar yau aƙalla mutane bakwa aka ciro daga ƙasan ginin shida daga cikin su basa iya motsa jikin su, yayin da hukumomi suka ci gaba da gudanar da aikin ceto sauran mutanen da ginin ya danne.

Continue Reading

Manyan Labarai

Sulhu da ƴan Bindiga ba zai haifar da Ɗa mai ido ba – Human Rights 

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta ƙasa da ƙasa wato International Human Rights Commission, ta ce sulhu da ƴan bindiga ba zai haifar da Ɗa mai ido ba a ƙasar nan.

Babban daraktan ƙungiyar Kyaftin Abdullahi Bakoji Adamu mai ritaya, shi ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano.

Ya ce kasancewar ƴan bindigar basu da wata manufa bai kamata ayi sulhu da su ba, mai-makon hakan yafi dacewa a rinƙa ɗaukar tsauttsauran mataki akan su duba da yadda suke cutar da al’umma.

Ya kuma ce batun da mai bai wa shugaban ƙasa akan sha’anin tsaro Malam Nuhu Ribaɗo, ya yi a baya baya nan, kam cewar an fara samun fashimtar juna da wasu daga cikin ƴan Bindigar da suka addabi mutane a sassan ƙasar nan, a wani ɓangare ma kama da yin sulhu da su, ya faɗi hakan ne kawai amma hakan ba zai haifar da Ɗa mai ido ba.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gwamnatin Kano ta kulle wata makaranta mai zaman kan ta a jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta rufe wata makaranta mai suna Golden Crown International School a jihar, da ke yankin Sabon gari, bisa zargin an fake da sunan makarantar ana haɗa magani mara inganci mai-makon koyar da karatu a ciki.

Shugaban kwamitin yaki da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya na jihar Kano General Gambo Mai Aduwa Mai ritaya, ne ya bayyana hakan, a lokacin da Kwamitin ya kai wani sumame da karfe uku da rabi na daren jiya Talata.

Rahotanni sun bayyana cewa makarantar tana kan titin Zungero da ke cikin ƙaramar hukumar Fagge a jihar Kano, wanda bayan samun bayanan sirri aka ɗauki matakin kulle ta.

Mai Aduwa, ya ƙara da cewar tsarin gurin ta waje ya nuna makaranta ce amma kuma sai ake sarrafa magani da ake zargin ingancin sa da bai kai yadda ya kamata ba, tare da ajiye Allurai da kayan haɗa magani cikin ajujuwan mai-makon ɗalibai.

“Za mu faɗaɗa bincike akan al’amarin dan sanin matakin da za mu ɗauka na gaba, “in ji shi”.

Suma masu gadin gurin da muka zanta da su sun bayana cewar, aikin gadi kawai suke yi amma basu da masaniyar abubuwan dake gudana a cikin makarantar, da ake zargin ana sarrafa magani mara ingani da ajiye shi a muhalin da ake zargin bai yi dai-dai da tsarin doka ba.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad ya rawaito cewa shugaban kwamitin ya ce, zai ci gaba da bibiyar guraren dake yin abubuwan da za su kawo koma baya ga harkokin lafiya, da ci gaban jihar Kano, musmman wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya.

Continue Reading

Trending