Connect with us

Labarai

Iyaye ku dai ma marawa ƴaƴan ku baya akan abinda suke yi da ya saɓawa doka – Mai unguwar Ja’en Jigawa

Published

on

Mai unguwar Ja’en Jigawa da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano Sani Muhammad, ya ce bai kamata a rinƙa samun wasu iyaye da ɗabi’ar nan ta marawa ƴaƴan su baya akan abinda yaran suke aikatawa na saɓawa Doka, domin gujewa abinda ka je ya dawo.

Mai unguwar ya bayyana hakan ne yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a lokacin da yake tsokaci kan yadda ake samun wasu daga cikin iyayen yankin sa na marawa ƴaƴan su baya kan abinda suke yi na ba dai dai ba, lamarin da yake ƙara ƙara kangarar da tarbiyyar ƴaƴan tare da tayar da hankalin al’umma.

Mai unguwa Sani Muhammad, ya kuma ce matuƙar yaran ba za su zauna lafiya a cikin unguwa da al’umma ba, to kuwa za su rinƙa ɗaukar matakin miƙa yaran hannun jami’an tsaro mafi kusa, domin ɗaukar matakin da ya dace a kan su, wajen ganin sun sauke nauyin da aka ɗora musu.

Sani Muhammad, ya ƙara da cewa ko a baya bayan nan wasu matasa sai da suka yi yunƙurin yin abinda bai kamata ba, lamarin da yasa aka ɗauki mataki a kansu amma aka samu wasu daga cikin iyaye suka marawa yaran nasu baya, wanda hakan kan haifar da barazanar tsaro.

Labarai

Dilolin Wiwi sun yanki mai unguwa da Wuƙa, tare da cizon shi a hannu, kan ya shana su sha da siyar da wiwi a Kano

Published

on

Wasu matasa da ake zargin ƴan Daba ne, kuma dilolin Wiwi, sun kai wa mai unguwar yankin Bachirawar Tukwane ƙarshen kwalta hari da muggan makamai.

Tun farko dai mai unguwar yankin Malam Mustapha ya shawarci matasan ne, da su dai na ɗaurin tabar Wiwi, da siyar wa a kofar gidajen mutane lamarin da ya tunzura matasan.

Matasan dai sun rutsa mai unguwar Bachirawar ne inda suka yi yunƙurin hallaka shi, bayan da suka yanke shi da Wuƙa, tare da cizon sa a Hannu, sai dai ‘yan ƙungiyar bijilante na yankin sun kawo masa ɗauki inda suka kama wani matashi mai laƙabin Kokuwa.

A lokacin ne kuma mutanen yankin suka yi yunƙurin ɗaukar doka a hannu, sai dai mai unguwar Bachirawa Malam Mustapha dan Bachirawa Gabas Malam Abdulkadir Dandiyo, sun kuɓutar da matashin inda aka mika shi ofishin ƴan sanda, ragowar matasan suka tsere.

Shugaban kungiyar ci gaban al’ummar yankin Dakta Jibrin Sagir, ya ce a shirye suke su tinkari duk wani ɓata gari a yankin da yake addabar su.

Continue Reading

Labarai

Mata ku ƙara kula da tsaftar jikin ku a gidan auren ku – DCG Dr. Khadijah Sagir Sulaiman

Published

on

Mataimakiyar babban kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano a ɓangaren Mata, DCG Dakta Khadijah Sagir Sulaiman, ta shawarci matan aure da su ƙara kulawa da tsaftar jikin su musamman kan abinda ya shafi bakunansu, da kuma gaɓoɓin da suke riƙe Gumi a wannan yanayi na zafi da ake ciki.

Dakta Khadijah Sagir, ta bayyana hakan ne yayin rangadin bibiyar auren gatan da gwamnatin jihar Kano ƙarkashin Injiniya Abba Kabir Yusuf, tayi a baya, wanda ta fara da ƙaramar hukumar Dawakin Kudu a jiya Lahadi, ina zaman ya gudana a ofishin Hisbah na ƙaramar hukumar.

DCG Khadijah, ta kuma ce matuƙar matan auren za su ƙara kulawa da tsaftar jikin nasu, hakan ka iya taimaka musu wajen ƙara wanzuwar zaman lafiya a tsakanin su da mazajen su.

Da take nata jawabin mataimakiyar kwamandan Hisbah ta ƙaramar hukumar Dawakin Kudu a ɓangaren mata Malama Saratu Sheikh Nasiru Kabara, cewa ta yi, ziyarar rangadin abu ne da tayi farin ciki, kasancewar bata taɓa samun makamanciyar ziyarar ba sama da shekaru 15 da fara aikin ta a can.

Wakiliyarmu Hadiza Balanti Ceɗiyar ƴan Gurasa ta rawaito cewa, yayin ziyarar rangadin bibiyar auren gatan Dakta Khadijah Sagir Sulaiman, ta kuma rarraba wa matan auren kayan goge baki, da kuma abubuwan da ke ɗauke sansanar jiki mara daɗi wato alumun, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Labarai

Kwamitin bincike kan tsohuwar gwamnatin Ganduje ya fara zama.

Published

on

Kwamitin da gwamnatin jahar kano ta kafa dan binciken gwamnatin Ganduje, ya bayyana irin sigar da masu korafi za su gabatar da ƙorafi a gaban kwamitin.

Gwamnatin jahar kano ta kafa kwamitin karkashin jagorancin mai Shari’a Faruk Lawan, dan bincike akan zargin da gwamnati mai ci take yiwa gwamnatin da ta shude akan yadda akayi tasarrafi da dukiyar jahar Kano.

A yayin zaman kwamitin mai Shari’a Faruk Lawan, ya bayyana cewa duk wani mai korafi zai rubuto korafinsa a takadda, domin gabatar wa a gaban kwamitin.

Gwamnatin dai ta kafa kwamatoci guda 2 dan bincike akan yadda akayi tassarifi da dukiyar jahar kano, da kuma abin da ya janyo ɓatan ƙananan yara, da rikice-rikicen siyasa wadanda akayi zargin sun faru a tsawon shekaru takwas na gwamnatin Ganduje.

Continue Reading

Trending