Connect with us

Manyan Labarai

Kantomomi, Malamai, da masu riƙe da masarautun gargajiya na Kano ta tsakiya sun yi mubaya’a ga Sarkin Kano Muhammadu Sunusi na biyu

Published

on

Shugabannin riƙo na ƙanananan hukumomi 15 na Kano ta tsakiya, malamai da dukkanin masu riƙe da masarautun gargajiyar yankin, sun yi mubaya’a ga Sarkin Kano Mallam Muhammadu Sunusi na biyu, tare da nuna goyon bayan su a gareshi.

Shugabannin riƙon na ƙananan hukumomin, da hakimai, da Malamai, da kuma Dagatai, da masu unguwanni, na Kano ta tsakiya, sun yi mubaya’ar ne yayin da suka ziyar ci fadar mai martaba sarkin Kano na 16, Mallam Muhammadu Sunusi na biyu, ranar Asabar a fadar sa.

Da yake jawabi ga Dala FM Kano, jim kaɗan da yin mubaya’ar, shugaban ƙungiyar shugabannin riƙo na ƙananan hukumomin Kano 44, kuma shugaban ƙaramar hukumar Tarauni Abdullahi Ibrahim Bashir, (Mai Kano) ya ce sun yi mubaya’ar ne bisa yadda mai martaba sarkin Kano Muhammadu Sunusi, yake da kishi da son ci gaban al’umma.

A nasa jawabin mai martaba sarkin Kano Mallam Muhammadu Sunusi na biyu, ya hori, shugabannin ƙananan hukumomin na Kano ta tsakiya, Malamai, da Hakimai, da Dagatai, da kuma masu unguwannin, da su mayar a hankali wajen samar da ci gaban al’umma.

Wannan dai na zuwa ne bayan da mai martaba sarkin Kano Muhammadu Sunusi na biyu, ya karɓi takardar kama aiki a ranar Juma’a 24 ga watan mayun 2024, bayan da gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a dokar masarautun da majalisar dokokin jihar suka yi wa kwaskwarima, wadda ta rushe sarakuna biyar a jihar Kano.

Tsohuwar gwamnatin Ganduje ce dai ta samar da dokar kafa masarautun jihar Kano biyar a shekarar 2019, wanda yanzu haka ta zama tarihi bayan da majalisar dokokin jihar ta yi mata kwaskwarima.

Manyan Labarai

Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Published

on

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.

Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.

Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.

A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.

Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Published

on

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.

“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.

Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.

Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.

Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.

Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Trending