Connect with us

Manyan Labarai

Ɗakin wasu matasa da ɗakin Girki a wani Gida sun ƙone ƙurmus a Kano

Published

on

Wata Gobara da ta tashi ta kone ɗakin kwanan wasu matasa da kuma ɗakin girki ƙurmus, a wani gida da ke gidan Maza a karamar hukumar Birni da ke jihar Kano, tare da asarar tarin dukiyoyi.

A zantawar wakilinmu Ibrahim Abdullahi Soron Dinki da matar gidan mai suna Mariya Ishak, ta ce gobarar ta tashi ne yau sakamakon kawowar wutar lantarki, al’amarin da yasa dukkanin kayayyakin da suke cikin ɗakunan suka ƙone ƙurmus.

Ta ce kayayyakin da suka ƙone sun haɗar da kayan sawar matasan da kuma Katifu, da sauran kayayyaki, wanda a lokacin da wutar ta tashi matasan sun tafi harkokin kasuwancin su.

Sai dai matar ta ce da taimakon mazauna yankin ne aka samu nasarar kashe gobarar ba tare da ta tsallaka sauran ɓangarori ko kuma tsallakawa makotan su ba, kuma ba a samu asarar rayuka ko rauni ba.

Akan al’amarin ne wakilin Dala FM Kano Hassan Mamuda Ya’u, ya zanta da mai magana da yawun hukumar kashe Gobara ta jihar Kano, PFS Saminu Yusif Abdullahi, inda ya ce akwai bukatar al’umma su rinka kiyayewa wajen amfani da kayayyakin wuta domin kaucewa tashin Gobara a muhallan su.

Ya kuma yi kira ga al’umma da cewa, duk lokacin da aka dauke wutar lantarki su tabbata sun kashe makunnin wato Soket, kafun dawowar wutar lantarkin domin gujewa tashin Gobara.

Manyan Labarai

Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu ya naɗa Hakimai Shida

Published

on

Mai martaba sarkin Kano Dakta Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, ya naɗa hakimai shida da safiyar Juma’ar nan tun bayan dawo da shi a matsayin Sarki.

Sarkin ya naɗa Alhaji Abba Yusuf baffan gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf a matsayin Ɗan Makwayon Kano, da Alhaji Auwalu Mudi Yakasai, shi kuma Ɗan Malikin Kano, da Abdulƙadir Muhammad Balarabe a matsayin Zannan Kano.

Sauran sune Alhaji Muhktar Ibrahim Bello da Sarkin ya naɗa shi a matsayin Falakin Kano, sai kuma Alhaji Aminu Abdullahi Nasidi a matsayin Galadiman Kano.

Wakilin Dala FM Kano Yakubu Ibrahim Doragarai ya ruwaito ya ruwaito cewa, tuni hakiman da aka naɗa suka yi gaisuwa ga Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin Kano da wani Kwamishina

Published

on

Jam’iyyar NNPP ta jihar Kano ta bayyana dakatar da sakataren gwamnatin jihar Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da Kwamishinan Sufuri na jihar Kano Muhammad Diggwal, daga cikin jam’iyyar.

Shugaban jam’iyyar NNPP a Kano Dakta Hashim Sulaiman Dungurawa ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a cikin daren yau Litinin.

Hashim Dungurawa, ya ce dakatar da ƙusoshin gwamnatin jihar Kano su biyu ya biyo bayan zargin keta alfarmar jagoranci, da ta Jam’iyya, da kuma keta alfarmar gwamnati, a don haka ne suka ɗauki matakin ba tare da yin wasa ba akai.

“Jagorancin shugabancin jam’iyyar mu na ƙananan hukumomin da mutane biyun suka fito sun gabatar mana da ƙorafe-ƙorafe kan ƙusoshin gwamnatin biyu, akan zarge-zarge da ake musu ya sa muka ɗauki matakin dakatar da su, har sai mun gama bincike, “in ji Dungurawa”.

Sulaiman ya ƙara da cewar dakatar da Abdullahi Baffa Bichi da Muhammad Diggwal ta fara aiki ne daga ranar Litinin 14 ga watan Oktoban 2024, kamar yadda jam’iyyar ta samu ingantattun shawarwari akan zargin da ake musu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ku tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa na Ɗorayi bisa halin da suke ciki – Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam 

Published

on

Ƙungiyar wayar da kan jama’a da kare haƙƙin ɗan adam da tallafawa mabuƙata, ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, ta tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa da ke unguwar Ɗorayi, da dafaffen abinci, domin rage musu wata damuwa.

Ƙungiyar dai ta rabawa masu lalurar Ƙwaƙwalwar abincin ne da yammacin Asabar 12 ga watan Oktoban 2024, tare da ziyartar wata makarantar tsangaya da ke unguwar Ɗorayi, inda ɗalibai 1,000 suka rabauta da tallafin dafaffen abincin.

Da yake yiwa Dala FM Kano, ƙarin bayani daraktan ƙungiyar ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, Kwamared Auwal Usman, ya ce rahotannin da suka samu kan yadda mazauna Asibitin da kuma makarantun tsangayar ke fuskantar ƙalubalen abinci ya sa suka kai musu tallafin domin rage musu wani raɗaɗi.

 

Wasu daga cikin masu lalurar Ƙwaƙwalwar da suka fara samun sauƙi, sun nemi ɗaukin gwamnatin jihar Kano wajen magance ƙalubalen da suke fuskanta na rashin kyawun wuraren da suke kwana da sauran matsaloli, ko sa samu wani sauƙi.

Da yake nasa jawabin mai kula da Asibitin da ake kula da masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi a Kano, Munnir Ɗahiru Kurawa, ya miƙa godiyar sa ga tawagar ƙungiyar bisa kaɓakin alkhairin da ta saukewa masu taɓin hankalin.

Wannan dai na zuwa ne makwanni kaɗan da gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ziyarci Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi, har ma ya bada umarnin aje a gyara shi, sai dai kawo yanzu hakan bata samu ba kamar yadda wata majiya ta bayyana.

Continue Reading

Trending