Manyan Labarai
Ɗakin wasu matasa da ɗakin Girki a wani Gida sun ƙone ƙurmus a Kano

Wata Gobara da ta tashi ta kone ɗakin kwanan wasu matasa da kuma ɗakin girki ƙurmus, a wani gida da ke gidan Maza a karamar hukumar Birni da ke jihar Kano, tare da asarar tarin dukiyoyi.
A zantawar wakilinmu Ibrahim Abdullahi Soron Dinki da matar gidan mai suna Mariya Ishak, ta ce gobarar ta tashi ne yau sakamakon kawowar wutar lantarki, al’amarin da yasa dukkanin kayayyakin da suke cikin ɗakunan suka ƙone ƙurmus.
Ta ce kayayyakin da suka ƙone sun haɗar da kayan sawar matasan da kuma Katifu, da sauran kayayyaki, wanda a lokacin da wutar ta tashi matasan sun tafi harkokin kasuwancin su.
Sai dai matar ta ce da taimakon mazauna yankin ne aka samu nasarar kashe gobarar ba tare da ta tsallaka sauran ɓangarori ko kuma tsallakawa makotan su ba, kuma ba a samu asarar rayuka ko rauni ba.
Akan al’amarin ne wakilin Dala FM Kano Hassan Mamuda Ya’u, ya zanta da mai magana da yawun hukumar kashe Gobara ta jihar Kano, PFS Saminu Yusif Abdullahi, inda ya ce akwai bukatar al’umma su rinka kiyayewa wajen amfani da kayayyakin wuta domin kaucewa tashin Gobara a muhallan su.
Ya kuma yi kira ga al’umma da cewa, duk lokacin da aka dauke wutar lantarki su tabbata sun kashe makunnin wato Soket, kafun dawowar wutar lantarkin domin gujewa tashin Gobara.

Baba Suda
Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.
Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.
Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Manyan Labarai
Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.
Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.
Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.
Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Manyan Labarai
Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.
Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su