Connect with us

Manyan Labarai

Mun kama matashin da ya yi garkuwa da wata yarinya ya nemi miliyan biyu matsayin kudin fansa a Kano – Ƴan Sanda

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta tabbatar da cafke wani matashi mai suna Zakariyya Muhammad, Ɗan shekara 22, mazaunin unguwar Sabuwar Gandu kwarin Barka a jihar, bisa zargin sa da laifin garkuwa da wata ƙaramar yarinya mai suna Amina ƴar shekara biyu da rabi, tare da neman Naira milyan biyu a matsayin kuɗin
fansa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya aikowa gidan rediyon Dala FM, a yau Talata 09 ga watan Yulin 2024.

Ya ce bayan samun rahoton yin garkuwa da yarinyar ne kwamishinan ƴan sandan Kano CP Salman Dogo Garba, ya bada umarni ga jami’an su domin kuɓutar da yarinyar tare da kama wanda ake zargi da garkuwa da ita.

Ya ci gaba da cewa, ba tare da ɓata lokaci ba jami’an nasu suka samu nasarar cafke matashin, yana mai cewa yanzu haka matashi Zakariyya Muhammad, yana babban sashin binciken manyan laifuka da ke hedikwatar ‘yan sandan da ke Bombai, ana faɗaɗa bincike, kuma da zarar an kammala za’a gurfanar dashi a gaban kotu domin girbar abin da ya shuka.

Da yake ƙarin bayani wanda ake zargi da yin garkuwa da yarinyar mai suna Zakariyya Muhammad, ya ce bayan da ya dauki yarinyar ne ya nemi Naira
milyan biyu a matsayin kuɗin fansa, ko da dai ya nuna nadamar sa bayan
da ya shiga hannun jami’an tsaron.

Shima mahaifin yarinyar da aka yi garkuwa da itan ya magantu, inda ya ce
ya yi mamaki kan yadda wanda ya sace ƴar tasa suka ga makocin su ne.

A cewar sa, “kafin ɗauke ƴar tamu sai da matashin yazo ya rubuta min lambar wayar sa, inda bayan ɗauke ƴar tamu ne aka rinƙa kiran waya tare da sanar mana cewar zamu bayar da Naira Miliyan biyu a matsayin kuɗin fansa, bayan mun kai ƙara aka bibiya inda aka kamo matashin, ƴar mu kuma yana cikin ƙoshin lafiya, “in ji shi”.

Daga bisani dai rundunar ‘yan sandan jihar Kanon ta kuma ja hankalin iyaye da su kara lura da ya’yan su, inda ta kuma gargadi matasa da su kaucewa sanya kan su cikin halin aikata munanan ayyuka, domin gudun faɗawa komar jami’an tsaro.

Manyan Labarai

Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu ya naɗa Hakimai Shida

Published

on

Mai martaba sarkin Kano Dakta Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, ya naɗa hakimai shida da safiyar Juma’ar nan tun bayan dawo da shi a matsayin Sarki.

Sarkin ya naɗa Alhaji Abba Yusuf baffan gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf a matsayin Ɗan Makwayon Kano, da Alhaji Auwalu Mudi Yakasai, shi kuma Ɗan Malikin Kano, da Abdulƙadir Muhammad Balarabe a matsayin Zannan Kano.

Sauran sune Alhaji Muhktar Ibrahim Bello da Sarkin ya naɗa shi a matsayin Falakin Kano, sai kuma Alhaji Aminu Abdullahi Nasidi a matsayin Galadiman Kano.

Wakilin Dala FM Kano Yakubu Ibrahim Doragarai ya ruwaito ya ruwaito cewa, tuni hakiman da aka naɗa suka yi gaisuwa ga Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin Kano da wani Kwamishina

Published

on

Jam’iyyar NNPP ta jihar Kano ta bayyana dakatar da sakataren gwamnatin jihar Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da Kwamishinan Sufuri na jihar Kano Muhammad Diggwal, daga cikin jam’iyyar.

Shugaban jam’iyyar NNPP a Kano Dakta Hashim Sulaiman Dungurawa ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a cikin daren yau Litinin.

Hashim Dungurawa, ya ce dakatar da ƙusoshin gwamnatin jihar Kano su biyu ya biyo bayan zargin keta alfarmar jagoranci, da ta Jam’iyya, da kuma keta alfarmar gwamnati, a don haka ne suka ɗauki matakin ba tare da yin wasa ba akai.

“Jagorancin shugabancin jam’iyyar mu na ƙananan hukumomin da mutane biyun suka fito sun gabatar mana da ƙorafe-ƙorafe kan ƙusoshin gwamnatin biyu, akan zarge-zarge da ake musu ya sa muka ɗauki matakin dakatar da su, har sai mun gama bincike, “in ji Dungurawa”.

Sulaiman ya ƙara da cewar dakatar da Abdullahi Baffa Bichi da Muhammad Diggwal ta fara aiki ne daga ranar Litinin 14 ga watan Oktoban 2024, kamar yadda jam’iyyar ta samu ingantattun shawarwari akan zargin da ake musu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ku tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa na Ɗorayi bisa halin da suke ciki – Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam 

Published

on

Ƙungiyar wayar da kan jama’a da kare haƙƙin ɗan adam da tallafawa mabuƙata, ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, ta tallafawa mazauna Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwa da ke unguwar Ɗorayi, da dafaffen abinci, domin rage musu wata damuwa.

Ƙungiyar dai ta rabawa masu lalurar Ƙwaƙwalwar abincin ne da yammacin Asabar 12 ga watan Oktoban 2024, tare da ziyartar wata makarantar tsangaya da ke unguwar Ɗorayi, inda ɗalibai 1,000 suka rabauta da tallafin dafaffen abincin.

Da yake yiwa Dala FM Kano, ƙarin bayani daraktan ƙungiyar ta Awareness for Human Right and Charity Foundation, Kwamared Auwal Usman, ya ce rahotannin da suka samu kan yadda mazauna Asibitin da kuma makarantun tsangayar ke fuskantar ƙalubalen abinci ya sa suka kai musu tallafin domin rage musu wani raɗaɗi.

 

Wasu daga cikin masu lalurar Ƙwaƙwalwar da suka fara samun sauƙi, sun nemi ɗaukin gwamnatin jihar Kano wajen magance ƙalubalen da suke fuskanta na rashin kyawun wuraren da suke kwana da sauran matsaloli, ko sa samu wani sauƙi.

Da yake nasa jawabin mai kula da Asibitin da ake kula da masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi a Kano, Munnir Ɗahiru Kurawa, ya miƙa godiyar sa ga tawagar ƙungiyar bisa kaɓakin alkhairin da ta saukewa masu taɓin hankalin.

Wannan dai na zuwa ne makwanni kaɗan da gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ziyarci Asibitin masu lalurar Ƙwaƙwalwar na Ɗorayi, har ma ya bada umarnin aje a gyara shi, sai dai kawo yanzu hakan bata samu ba kamar yadda wata majiya ta bayyana.

Continue Reading

Trending