Connect with us

Manyan Labarai

Mun kama matashin da ya yi garkuwa da wata yarinya ya nemi miliyan biyu matsayin kudin fansa a Kano – Ƴan Sanda

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta tabbatar da cafke wani matashi mai suna Zakariyya Muhammad, Ɗan shekara 22, mazaunin unguwar Sabuwar Gandu kwarin Barka a jihar, bisa zargin sa da laifin garkuwa da wata ƙaramar yarinya mai suna Amina ƴar shekara biyu da rabi, tare da neman Naira milyan biyu a matsayin kuɗin
fansa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya aikowa gidan rediyon Dala FM, a yau Talata 09 ga watan Yulin 2024.

Ya ce bayan samun rahoton yin garkuwa da yarinyar ne kwamishinan ƴan sandan Kano CP Salman Dogo Garba, ya bada umarni ga jami’an su domin kuɓutar da yarinyar tare da kama wanda ake zargi da garkuwa da ita.

Ya ci gaba da cewa, ba tare da ɓata lokaci ba jami’an nasu suka samu nasarar cafke matashin, yana mai cewa yanzu haka matashi Zakariyya Muhammad, yana babban sashin binciken manyan laifuka da ke hedikwatar ‘yan sandan da ke Bombai, ana faɗaɗa bincike, kuma da zarar an kammala za’a gurfanar dashi a gaban kotu domin girbar abin da ya shuka.

Da yake ƙarin bayani wanda ake zargi da yin garkuwa da yarinyar mai suna Zakariyya Muhammad, ya ce bayan da ya dauki yarinyar ne ya nemi Naira
milyan biyu a matsayin kuɗin fansa, ko da dai ya nuna nadamar sa bayan
da ya shiga hannun jami’an tsaron.

Shima mahaifin yarinyar da aka yi garkuwa da itan ya magantu, inda ya ce
ya yi mamaki kan yadda wanda ya sace ƴar tasa suka ga makocin su ne.

A cewar sa, “kafin ɗauke ƴar tamu sai da matashin yazo ya rubuta min lambar wayar sa, inda bayan ɗauke ƴar tamu ne aka rinƙa kiran waya tare da sanar mana cewar zamu bayar da Naira Miliyan biyu a matsayin kuɗin fansa, bayan mun kai ƙara aka bibiya inda aka kamo matashin, ƴar mu kuma yana cikin ƙoshin lafiya, “in ji shi”.

Daga bisani dai rundunar ‘yan sandan jihar Kanon ta kuma ja hankalin iyaye da su kara lura da ya’yan su, inda ta kuma gargadi matasa da su kaucewa sanya kan su cikin halin aikata munanan ayyuka, domin gudun faɗawa komar jami’an tsaro.

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Manyan Labarai

Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.

Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.

Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Published

on

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.

Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

Continue Reading

Trending