Manyan Labarai
Mun bai wa DSS, wa’adin awa ɗaya su saki shugaban mu ko aga matakin da zamu ɗauka – NLC

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa NLC, ta bai wa hukumar tsaron farin kaya ta DSS wa’adin awa guda da su saki shugaban su na ƙasa Joe Ajearo, ko kuma aga matakin da zai biyo baya daga gareta.
Sakataren tsare-tsaren ƙungiyar ta NLC, a matakin ƙasa Kwamared Nasir Kabir, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM a yammacin Litinin ɗin nan.
Ya kuma ce a lokacin da jami’an DSS, suka kama shugaban nasu a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe da ke Abuja, a dai-dai lokacin da zai tafi ƙasar Ingila, babu wata takardar umarnin kamu da suke tare da ita, kuma ƙungiyar ba za ta zuba ido ana zaluntar ƴan ƙasa su zuba idanu su ƙyale ba.
Kwamared Nasir Kabir ya kuma ƙara da cewa yanzu haka sun shiga wata tattaunawar gaggawa, domin samar da matsaya kan kamun da aka yiwa shugaban nasu.
Ƙungiyar ta kuma umartarci mambobin su da su kasance a cikin shirin ko ta kwana kan mataki da za su ɗauka matuƙar ba’a saki shugaban nasu ba, inda ya bukaci kada ƴan Najeriya suji haushin su kan matakin da za aga sun ɗauka bisa zalunci da aka yiwa ƴan ƙasa.
“Yanzu haka mun sanarwa dukkanin mambobin mu na jahohi 36 da Abuja, da su kasace cikin shirin ko ta kwana, da kuma duk manyan ƙungiyogin mu da suka shafi wutar lantarki, da na man Fetur, da makarantu da sauransu, “in ji shi”
Da safiyar Litinin ɗin nan ne dai jami’an tsaron farin kaya na DSS suka kama shugaban ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa NLC, Joe Ajearo, a lokacin da yake shirin barin ƙasar domin tafiya ƙasar Ingila, don halartar taron da aka gayyaceshi na inganta rayuwar ma’aikata da sauran abubuwan more rayuwar su.

Baba Suda
Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.
Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.
Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Manyan Labarai
Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.
Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.
Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.
Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Manyan Labarai
Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.
Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su