Manyan Labarai
Kitumurmurar da gwamnatin Tinubu take shiryawa jihar mu ba za ta yi tasiri ba – Gwamantin Kano

Gwamnatin jihar Kano ta ce babu wata matsalar tsaro a ko kuma shirin tayar da hargitsi a jihar, da aka rinƙa yadawa cewar za a iya samu a jihar.
Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudanar cikin daren juma’ar nan ta 24 ga watan Janairun 2025.
Ya ce rahotannin da ake yaɗawa cewar za a iya samun tayar da hargitsi daga wasu ƴan ta’adda a jihar, gwamnatin jihar Kano bata da masaniya akan batun, kuma lamarin bashi da tushe ballantana makama.
“An zo an jibge jami’an tsaron ƴan sandan gwamnatin tarayya a mashigar filin wasa na Sani Abacha Stadium, da sunan za a hana Maulidin da aka saba gabatarwa duk shekara, wanda aka shirya gudanarwar a gobe Asabar, inda jami’an tsaron ke neman hanawa, kuma ba zamu mu amince da hakan ba, “in ji Waiya”.
A cewar sa, Kitumurmurar da gwamnatin shugaba Bola Tinubu take shiryawa jihar Kano ba za ta yi tasiri ba.
Wanan dai na zuwa ne bayan da rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta bakin kakakin ta SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ta sanar da cewar, ta samu bayanan sirri kan yadda wasu ɓata gari ke shirin tarayyar da tarzoma jihar Kano, al’amarin da gwamantin jihar ta musanta.

Baba Suda
Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.
Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.
Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Manyan Labarai
Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.
Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.
Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.
Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Manyan Labarai
Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.
Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su