Connect with us

Manyan Labarai

Cinikin jariri ya bar baya da kura Kano.

Published

on

Wata Ungozoma Mai suna Tambai Sani ta tsinci kanta cikin badakala, sakamakon zargin da akayi mata na karbar haihuwa, da yunkurin jefanar da jaririyar da aka haifa.

Ba ta hanyar aure aka same shi ba.

Wata Matashiya Mai Suna Fatima Sulaiman dake Hotoro unguwar Kujama ce ta haifi jaririn da aka hakkake ba’a same shi ta hanyar aure ba, kafin daga bisani labari ya sauya.

Wata shaida kan abinda ke faruwa ta shaidawa jakadan mu Abba Isa cewa bacewar basirar yadda za’ayi da jaririn ya sanya ungozomar zuwa da masalaha, cewar idan anason sayarwa tana da masu saya a hannu.

An fara ciniki.

Taya kwabo albarka akayi cinikin jariri har yawan kudi ya kai naira Dubu Saba’in cif-cif. Sai dai abinka da sha’ani na rashin gaskiya cinikin ya yiwu, saai dai kuma wacce amsa za’a baiwa mutanen unguwa akan inda jaririn ya shiga, tunda dai ba mutuwa yayi ba?

Kifi na ganinka.

Tun gabanin lalubo hanyar da za’a binne abin kunyar yan Unguwa suka samu cikakken rahoto, tare da tashin cinikin da ake zargin an kullashi a boye.

Yanzu haka dai magana tayi nisa inda jami’an tsaro suka karbi bayanan mutanen unguwa da cikakkun hujjojin takardun cinikayya, har suka baza koma wajen zabarin wadanda ake zargin kulla harkallar.

Muna da hanzari.

Mahaifiyar Buduruwar Mai suna Adama Sulaiman tace kyauta suka yi da sambaleliyar jaririyar ga wata mata mai suna Kadija Usman, da Allah bai bata haihuwa ba.

Daga bisani Jakadan namu Abba Isah Muhammad ya tuntubi Kakakin Rundunar Yansandan Jihar Kano DSP Abdullahi Haruna wanda ya tabbatar da wannan al’amari da tuni ke gabansu domin bincike da tabbatar wa mai laifi laifinsa.

Ko da yake ya zuwa yanzu bai yi karin hasken ko an samu wadanda ke da hannu wajen wannan cinikayya, da ta kasance haramun a dokar Najeriya.

Manyan Labarai

Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Published

on

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.

Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.

Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.

A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.

Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Published

on

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.

“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.

Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.

Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.

Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.

Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Trending