Connect with us

Labarai

Yadda zaman majalisar dokokin jihar Kano ya gudana a yau

Published

on

An bukaci gwamnatin jihar Kano Samar da hanyar da ta tashi daga sabon garin Wudil zuwa kasuwar Garko dukkanin su a kananan hukumomin Garko da Wudil dake jihar kano.

Wannan ya biyo bayan wani kudurin hadin gwiwa da yan majalissun kananan hukumomin biyu suka gabatar a zauren majalissar dokokin jihar ta Kano wato Abba Ibrahim Garko da takwararsa na wudil Nuhu Abdullahi Achika.

Inda suka ce Samar da wannan hanya zai  taimaka wajen habaka tattalin arzikin al’ummomin yankunan biyu.

RUBUTU MASU ALAKA:

Majalisa: A gaggauta dawo da yaran da aka sace

Majalisa ta amince ta ginin titunan Kano zuwa Katsina

A dai zaman majalissar dokokin jihar ta Kano na yau Dan majalissar dokokin jihar kano mai wakiltar karamar hukumar Kumbotso Mudassir Ibrahim Zawachiki ya bukaci gwamnatin jihar Kano data Samar da hanyar data tashi daga Na’ibawa bye pass zuwa yan Shana sannan kuma da hanyar Yangizo zuwa Garu dakuma ta Limawa duk a karamar hukumar sa ta Kumbotso.

Bayan gabatar da muhawara akan wadannan kudurori ne dai majalissar dokokin jihar kano karkashin jagorancin Abdulaziz Garba Gafasa ta amince da wadannan kudurori.

KARANTA WANNA:

Mun shirya tsaf don kare cin zarafin yara -Kakakin majalisar yara

Haka zalika majalissar dokokin jihar kano ta amince da Nada Maifada Bello Kibiya a matsayin mamba mai daraja ta daya a hukumar amintattu masu kula da asusun yan fansho ta jihar kano.

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoto da shugaban kwamitin kula da hukumar Fansho ta jihar kano a zauren majalissar dokokin jihar kano Kabiru Yusuf Ismail’ daga karamar hukumar Madobi yayi a zauren majalissar, inda yace kwamitin yayi bincike kwarai akan Maifada sannan kwamitin ya tabbatar da kwarewarsa da jajircewar sa.

Wakiliyarmu ta majalisar dokokin jihar Kano Khadija Ishaq Muhammad ta rawaito cewa Majalissar dokokin jihar kano ta amince da dokar data amince domin kafa hukumar kula da al’amuran majalissar dokokin jihar Kano wadda aka yi ta tun a shekarar 2007 a zamanin tsohuwar gwamnatin Malam Ibrahim shekarau.

Wannan mataki ya biyo bayan bukatar da gwamnan jihar kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje yayi inda yace akwai bukatar ayi kwaskwarima akan sabuwar dokar da majalissar ta sake gabatarwa a shekarar 2018, Wanda hakan yasa majalissar ta amince da tsohuwar dokar ta shekarar 2007 mai makon ta 2018.

RUBUTU MAI ALAKA:

Majalisar dinkin duniya ta baiwa Sarkin Kano mukami

Majalissar dokoki ta yi zaman kara yawan sarakunan yanka a kano

Tsohuwar dokar dai tace kowa ka iya jagorantar hukumar matukar yana da kwarewa a aikin majalissar maimakon sabuwar datace lallai sai Wanda ya taba kasancewa Dan majalissa.

Bayan kammala tattaunawa ne kuma shugaban majalissar dokokin jihar Kano Abdulaziz Garba Gafasa ya bukaci gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Dakta Abdullahi Umar Ganduje da ya gaggauta aiwatar da wannan dokar tare da rantsar da jagororin hukumar kula da al’amuran majalisar dokokin jihar Kano domin fara aiwatar da nauyin da aka Dora musu.

Labarai

Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.

Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Continue Reading

Labarai

Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.

Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.

“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.

Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.

Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Continue Reading

Labarai

Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Published

on

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.

Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.

Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.

Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

Continue Reading

Trending