Connect with us

Labarai

Rikici ya barke tsakanin ‘yan KAROTA da Sojoji

Published

on

dan KAROTA ya rasa ransa abakin aiki

Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano DSP Adullahi Haruna Kiyawa ya shaidawa Freedom Radio cewa, sojoji uku na hannun su sakamakon wata hatsaniya da ta barke a tsakanin su da jami’an KAROTA da tsakar ranar jiya a kan kwanar Kasuwar Sharada dake karamar hukumar Birni da Kewaye a nan Kano.

Sojojin dai sun baiwa hammata iska a yayin da hatsaniyar ta barke a tsakanin su har ta kai ga an sami rauni.

Yadda rikicin ya samu asali:

Rahotanni dai sun bayyana cewa rikicin dai ya samo asali ne sakamakon aron hannu da ake zargin Sojojin sun yi don raste hanya, duk kuwa da cewa ba hannunsu bane, wanda kuma hakan ya sabawa doka, dalilin kenan da ya sanya ‘yan KAROTAR suka tare su.

Wasu shaidun gani da ido sun bayyana mana cewa ana tsaka da musayar yawu ne wani daga cikin sojojin ya doki dan karotar a ka har ya fasa masa kai.

Ko da muka tuntubi hukumar KAROTA don jin ko me hukumar za ta ce, jami’in hulda da jama’a na hukumar Nabulisi Abubakar Kofar Na’isa ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce yanzu haka ma maganar tana hannun ‘yan sanda.

Haka zalika Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano DSP Adullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da cewa runduna na cigaba da bincike bayan da aka yi zargin cewar sojojin na cikin Adai-daita Sahu al’amarin ya afko

Wakilinmu Umar Lawan Tofa ya rawaito cewa rikicin ya fara ne daga Kwanar Kasuwar Sharada har ta kai zuwa kan titin Yahaya Gusau.a nan Kano.

 

 

 

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending