Connect with us

Labarai

Kai-tsaye : Mai shari’a Usman Na’abba ya yi hukuncin rushe kirkirar karin masarautu 4

Published

on

Babbar kotun jiha mai lamba 8 karkashin jagorancin mai shari’a Usman Na abba ta ayyana cewar dokar da majalisar dokoki tayi na baiwa gwamnatin kano damar kacaccala masarautar kano dokar haramtacciya ce.

Yayin da yake karanta hukuncin mai shari’a Na’abba ya bayyana cewar dukkanin sukar da gwamnati da majalisa suka yi a kunshin shariar ba su da tushe baki daya,

Ya kuma tabbatar da cewar dokar da majalisar tayi ba karbabbiya ba ce a don haka ya rushe dokar.

Tun da fari dai dan majalisar jiha mai wakiltar Gwarzo Hon Nasir Muhammad ne ya shigar da karar yana kalubalantar gwamnatin jiha da majalisar dokokin kano da kwamishinan Sharia akan cewar hanyar da majalisar ta bi a wajen yin dokar ba sahihiya ba ce.

Sai dai masu martani sun yi suka akan hurumin kotun tun a baya kotun ta kuma ayyana cewar tana da hurumin yin Shari’ar.

 

Jim kadan bayan kammala hukuncin mai shari’a Na abba ya bayyana cewar duk wanda hukuncin bai wa dadi ba zai iya daukaka kara.

Wakiln mu Yusuf Nadabo Isma’il ya zanta da lauyan masu kara Maliki Kuliya wanda yace daman dokar ta san rai ce.

Shi kuwa kwamishinan Sharia Ibrahim Muktar yace za su yi nazari akan hukuncin.

Babbar kotun jaha mai lamba 8 karkashin mai shari’ar Usman Na Abba ta fara karanta hukunci a kunshin shari’ar nan wadda Hon Nasir Muhammad ya shigar yana karar majalisar dokokin jahar ta jiha da gwamnan Kano da kuma babban baturen Sharia na jihar Kano, wato kwamishinan shari’a na jihar Kano Barrister Ibrahim Mukhtar.

Mai karar wanda tsohon dan majalisar dokokin Kano ne yana kalubalantar majalisar dokokin jihar nan bisa yadda yace ta saba ka’ida wajen yin dokar da ta baiwa gwamna damar  masarautar kano.

Raba Masarautar Kano: Umarnin kotu baizo mana akan lokaci ba -Sakataren gwamnatin Kano

Siyasantar da masaurata kawai ake son yi-Isyaku Ali Danja

A dai dai wannan lokaci mai shari’a Usman Na abba yana tsaka da karanta hukuncin kuma ana sa ran nan da Awa guda  kotun zata kammala karatun daga nan ta bayyana matsayar ta.

ku cigaba da bibiyar shafin don jin yadda shari’ar take gudana

Labarai

Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.

Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Continue Reading

Labarai

Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.

Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.

“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.

Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.

Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Continue Reading

Labarai

Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Published

on

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.

Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.

Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.

Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

Continue Reading

Trending