Connect with us

Labarai

Kai-tsaye : Mai shari’a Usman Na’abba ya yi hukuncin rushe kirkirar karin masarautu 4

Published

on

Babbar kotun jiha mai lamba 8 karkashin jagorancin mai shari’a Usman Na abba ta ayyana cewar dokar da majalisar dokoki tayi na baiwa gwamnatin kano damar kacaccala masarautar kano dokar haramtacciya ce.

Yayin da yake karanta hukuncin mai shari’a Na’abba ya bayyana cewar dukkanin sukar da gwamnati da majalisa suka yi a kunshin shariar ba su da tushe baki daya,

Ya kuma tabbatar da cewar dokar da majalisar tayi ba karbabbiya ba ce a don haka ya rushe dokar.

Tun da fari dai dan majalisar jiha mai wakiltar Gwarzo Hon Nasir Muhammad ne ya shigar da karar yana kalubalantar gwamnatin jiha da majalisar dokokin kano da kwamishinan Sharia akan cewar hanyar da majalisar ta bi a wajen yin dokar ba sahihiya ba ce.

Sai dai masu martani sun yi suka akan hurumin kotun tun a baya kotun ta kuma ayyana cewar tana da hurumin yin Shari’ar.

 

Jim kadan bayan kammala hukuncin mai shari’a Na abba ya bayyana cewar duk wanda hukuncin bai wa dadi ba zai iya daukaka kara.

Wakiln mu Yusuf Nadabo Isma’il ya zanta da lauyan masu kara Maliki Kuliya wanda yace daman dokar ta san rai ce.

Shi kuwa kwamishinan Sharia Ibrahim Muktar yace za su yi nazari akan hukuncin.

Babbar kotun jaha mai lamba 8 karkashin mai shari’ar Usman Na Abba ta fara karanta hukunci a kunshin shari’ar nan wadda Hon Nasir Muhammad ya shigar yana karar majalisar dokokin jahar ta jiha da gwamnan Kano da kuma babban baturen Sharia na jihar Kano, wato kwamishinan shari’a na jihar Kano Barrister Ibrahim Mukhtar.

Mai karar wanda tsohon dan majalisar dokokin Kano ne yana kalubalantar majalisar dokokin jihar nan bisa yadda yace ta saba ka’ida wajen yin dokar da ta baiwa gwamna damar  masarautar kano.

Raba Masarautar Kano: Umarnin kotu baizo mana akan lokaci ba -Sakataren gwamnatin Kano

Siyasantar da masaurata kawai ake son yi-Isyaku Ali Danja

A dai dai wannan lokaci mai shari’a Usman Na abba yana tsaka da karanta hukuncin kuma ana sa ran nan da Awa guda  kotun zata kammala karatun daga nan ta bayyana matsayar ta.

ku cigaba da bibiyar shafin don jin yadda shari’ar take gudana

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending