Connect with us

Labarai

An gurfanar da wani matashi a gaban kotu bisa zargin bata suna

Published

on

Kotun majistret mai lamba 15 karkashin mai Sharia Muntari Garba Dandago ta fara sauraron wata shari’a wadda ‘yan sanda suka gurfanar da wani mutum mai suna Abdulkadir Musa Guza.

Musa mazaunin unguwar Rijiyar Zaki ana zargin sa da lefin bata suna laifin da ya saba da sashi na 391 na kundin penal code.

Tun da farko wata mata mai suna Aisha Ibrahim Dankano ce ta shigar da kara bisa yanda ta zargi Musa Guza ya ce mata karuwa a yayin da suke taron Jam’iyyar su ta PRP.

Yayin da aka karanta kunshin tuhumar wanda ake karar ya musanta zargin.

Kuma lauyoyin sa Barrister Ibrahim Sa’adu Kura da Abdulkarim Maude Minjibir sun roki kotun da ta sanya shi a hannun beli.

Mai Shari’a Dandago ya sanya Guzan a hannun beli sai dai ya gindaya sharadin cewar sai mai matakin albashi na 15 ya tsaya masa idan kuma Guzan ya tsere mai karbar belin zai biya Naira dubu dari biyar.

Sai dai lauyan da yake kare Musa Guza Barrister Maude Minjibir ya bayyana cewar Guzan ba mai lefi bane zargi ne kawai ake masa.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya zanta da lauyan mai kara barister Hassan Tanko Kyaure wanda ya bayyana cewar za su gabatar da shaidu a gaban kotun.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending