Connect with us

Labarai

KAROTA bata da hurumin baiwa masu adai-daita sahu iznin tuki -Barista Rabi’u Sa’id

Published

on

Wani lauya mai rajin kare hakkin al’umma Barista Rabi’u Sa’id Rijiyar Lemo ya bayyana cewa hukumar KAROTA bata da hurumin baiwa masu baburan adai-daita sahu lasisin yin tuki, sannan kalaman shugaban hukumar Baffa Babba Dan’agundi kan yunkurin KAROTA akan direbobin adai-daita sahun kalamai ne da suka sabawa doka.

Idan zaku iya tunawa dai Baffa Babba ya ce zasu fara kwace baburan adai-daita sahun direbobin da basuyi rijista dasu ba daga farkon shekara mai kamawa ta 2020.

Sai dai Barista Rabi’u Sa’id ya ce dokar da Baffa Babba Dan’aguni ke magana akanta sam Baffan bai fahimci abinda take nufi ba, kuma abinda Baffa yayi furuci dashi ya saba da dokar hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa Road Safety da kuma hukumar lura da lafiyar ababan hawa ta kasa wato VIO, domin Road Safety kadai doka ta baiwa dama su bayar da lasisin yin tuki ba KAROTA ba.

Labarai masu alaka:

Hangen Dala: Zamuyi karar KAROTA a kotu idan ta kona adai-daita sahu -Auwalu Soja

KAROTA zata fara kwacen baburan adai-daita sahu a Kano

Kazalika Road Safety su ne aka baiwa dama su dauki bayanan mutum don su bashi lasisin tuki, sannan VIO sune ke da hurumin tambayar kana da lasisi ko baka da shi amma ko kadan ba hurumi ne na KAROTA ba a cewar Barista Rabi’u Sa’id.

Sannan dukkan takardu da ake baiwa masu amfani da ababan hawa babu daya da yake karkashin hukumar KAROTA.

A don haka Barista Rabi’u Sa’id ya ce sun shirya tsaf don maka hukumar KAROTA a kotu kan wannan batu.

Labarai

Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama

Published

on

Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.

Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.

Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.

Continue Reading

Labarai

Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam

Published

on

Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.

Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.

Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.

Continue Reading

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Trending