Labarai
FITACCEN LABARIN MAKO
Sandar majalisa wata alama ce ta iko wacce idan babu ita ba za’a iya gudanar da zaman majalisa ba.
Anshiga rudani acikin majalisar dattijai ta kasa a safiyar ranar laraba, 18,04,2018, yayin da wasu yan daba suka kutsa kai cikin majalisar domin dawo da dakataccen dan majalisa OVIE OMO AGEGE, yan daban sunyi amfani da karfi akan jami’an tsaro sannan suka dauke sandar majalisar da misalin karfe 11:30 na safe.
Maharan wanda yawansu yakai mutum goma sha biyar sunzo ne a motoci guda uku suka ajiyesu a gaban kofar majalisar tarayya, wasu daga cikinsu suka tsaya domin gadin kofar shiga majalisar tarayya, yayin da wasu suka tsaya suna gadin motocinsu, bayan misalin minti biyar da sauka da cikinsu motocinsu, mutane uku daga cikin yan daban suka shiga cikin majalisar suka fito da sandar majalisar suka shiga cikin motocinsu domin su tsere, yayin da sukazo fita ta kofar majalisar sai suka ga an rufeta, sai suka juya da baya suka fita ta kofar da ta hada majalisar tarayya da gidan shugaban kasa, wacce ake kira da “VILLA GATE” ta wannan kofar suka samu nasarar tserewa a guje.
Bayan lokaci kadan yan majalisar Dattaijai suka bude majalisar bayan sun rasa abin yine daga baya aka gane sun shiga mitin na gaggawa a sirrance.
A wannan rana da al’amarin ya faru mataimakin shugaban majalisar Eke okweremadu shi yake shugabantar majalisar, sakamakon shugaban majalisar Bokolo Saraki yana kasar amurka domin wakiltar taron bankin duniya da bankin tallafi na duniya.
Ovie Omo Agege sanata ne da yake wakiltar Dalta ta tsakiya a majalisar tarayya,kuma shine wanda ake zargi ya jagorancin shigar da yan daba cikin majalisar,a kokarinsu na dawo dashi majalisar bayan an dakatar dashi.
Gungun jami’an tsaro wanda kwamishinan yan sanda Sadik Abubakar Bello ya shugabanta ne zuwa cikin majalisar suka kama Sanata Ovie Omo Agege ta karfi, saidai sunyi artabu kafin su kamashi sakamakon goyon bayansa da wasu daga cikin yan majalisar sukayi, yan majalisar da suka nuna goyon bayansu ga Ovie Omo Agege sune; Sanata Nelson Effighem wanda yake wakiltar Akwa ibom, da Taiyo Alasadura wanda yake wakiltar Ape ta Ondo, da kuma Sanata Adrew Uchedu daga jihar Rivers.
A jawabin da mataimakin majalisar yayi acikin kwaryar majalisar yayi godiya ga sanatocin akan goyon bayan da suka bayar yayin faruwar al’amarin, yace, “A wannan safiyar abu wanda ba’a saba dashi ba ya faru da misalin karfe 11:30 na safe wasu yan daba sun kawo hari cikin majalisa , suka ci mutuncin wasu daga cikin ma’aikatan majalisa, da kuma wasu daga cikin manema labarai na yan jarida, sukayi amfani da karfi wajen dauke sandar majalisa,suka gudu, kuma sun gwada yunkurin yin garkuwa da biyu daga cikin Sanatocinmu, wannan cin mutunci ne ga Sanatoci da kuma Damakwaradiyya da majalisar tarayya gaba daya, amma zamu kasance tsintsiya daya wajen gabatar da aikin da yan kasa suka dora mana wajen wakiltarsu, zamu yi bincike wajen gano wannan matsalar,na tabbatar da cewa na fadi abinda yake zuciyar sauran yan majalisa”.
Bayan awa ashirin da hudu da faruwar al’amarin, Jami’an tsaro sun gano Sandar majalisar a hanyar fita daga garin Abuja inda yan daban suka yar dashi sakamakon tsaurara matakan tsaro da akayi acikin garin na Abuja.
Saidai wata kotu da take acikin garin Abuja ta haramtawa Jami’an tsaro kara kama Sanata Ovie Omo Agege har sai an tabbatar da zargin da ake yi masa.

Labarai
Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.
Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.
Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.
Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.
A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Labarai
Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.
Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.
“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.
Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.
Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Labarai
Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.
Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.
Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.
Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su