Connect with us

Labarai

FITACCEN LABARIN MAKO

Published

on

Sandar majalisa wata alama ce ta iko wacce idan babu ita ba za’a iya gudanar da zaman majalisa ba.

Anshiga rudani acikin majalisar dattijai ta kasa a safiyar ranar laraba, 18,04,2018,  yayin da wasu yan daba suka kutsa kai cikin majalisar domin dawo da dakataccen dan majalisa OVIE OMO AGEGE,  yan daban sunyi amfani da karfi akan jami’an tsaro sannan suka dauke sandar majalisar da misalin karfe 11:30 na safe.

Maharan wanda yawansu yakai mutum goma sha biyar sunzo ne a motoci guda uku suka ajiyesu a gaban kofar majalisar tarayya, wasu daga cikinsu suka tsaya domin gadin kofar shiga majalisar tarayya, yayin da wasu suka tsaya suna gadin motocinsu, bayan misalin minti biyar da sauka da cikinsu motocinsu, mutane uku daga cikin yan daban suka shiga cikin majalisar suka fito da sandar majalisar suka shiga cikin motocinsu domin su tsere, yayin  da sukazo fita ta kofar majalisar sai suka ga an rufeta, sai suka juya da baya suka fita ta kofar da ta hada majalisar tarayya da gidan shugaban kasa, wacce ake kira da “VILLA GATE” ta wannan kofar suka samu nasarar tserewa a guje.

Bayan lokaci kadan yan majalisar Dattaijai suka bude majalisar bayan sun rasa abin yine daga baya aka gane sun shiga mitin na gaggawa a sirrance.

A wannan rana da al’amarin ya faru mataimakin shugaban majalisar Eke okweremadu shi yake shugabantar majalisar, sakamakon shugaban majalisar Bokolo Saraki yana kasar amurka domin wakiltar taron bankin duniya da bankin tallafi na duniya.

Ovie Omo Agege sanata ne da yake wakiltar Dalta ta tsakiya a majalisar tarayya,kuma shine wanda ake zargi ya jagorancin shigar da yan daba  cikin majalisar,a kokarinsu na dawo dashi majalisar bayan an dakatar dashi.

Gungun jami’an tsaro wanda kwamishinan yan sanda Sadik Abubakar Bello ya shugabanta ne zuwa cikin majalisar suka kama Sanata Ovie Omo Agege ta karfi, saidai sunyi artabu kafin su kamashi sakamakon goyon bayansa da wasu daga cikin yan majalisar sukayi, yan majalisar da suka nuna goyon bayansu ga Ovie Omo Agege sune; Sanata Nelson Effighem wanda yake wakiltar  Akwa ibom, da Taiyo Alasadura wanda yake wakiltar Ape ta Ondo, da kuma Sanata Adrew Uchedu daga jihar Rivers.

A jawabin da mataimakin majalisar yayi acikin kwaryar  majalisar yayi godiya ga sanatocin akan goyon bayan da suka bayar yayin faruwar al’amarin, yace, “A wannan safiyar abu wanda ba’a saba dashi ba ya faru da misalin karfe 11:30 na safe wasu yan daba sun kawo hari cikin  majalisa , suka ci mutuncin wasu daga cikin ma’aikatan majalisa, da kuma wasu daga cikin manema labarai na yan jarida, sukayi amfani da karfi wajen dauke sandar majalisa,suka gudu, kuma sun gwada yunkurin yin garkuwa da biyu daga cikin Sanatocinmu, wannan cin mutunci ne ga Sanatoci da kuma Damakwaradiyya da majalisar tarayya gaba daya, amma zamu kasance tsintsiya daya wajen gabatar da aikin da yan kasa suka dora mana wajen wakiltarsu, zamu yi bincike wajen gano wannan matsalar,na tabbatar da cewa na  fadi abinda yake zuciyar sauran yan majalisa”.

Bayan awa ashirin da hudu da faruwar al’amarin, Jami’an tsaro sun gano Sandar majalisar a hanyar fita daga garin Abuja inda yan daban suka yar dashi sakamakon tsaurara matakan tsaro da akayi acikin garin na Abuja.

Saidai wata kotu da take acikin garin Abuja ta haramtawa Jami’an tsaro kara kama Sanata Ovie Omo Agege har sai an tabbatar da zargin da ake yi masa.

 

 

 

Labarai

Shugabanni ku fito da sabbin dabaru domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta tsadar rayuwa a ƙasa – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights dake jihar Kano, ta ce akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya dace dan ganin an kawo karshen matsalar tsaro, da kuma ta harkar tsaro dake ci gaba da addabar mutane a sassa ƙasar nan.

Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Laraba, ya ce yadda ake ƙara samun ƴan ta’adda suna sace mutane tare da kashe su a sassan ƙasar nan, da kuma halin matsin rayuwar da ake fuskanta akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya kamata dan ganin an kawo ƙarshen matsalolin.

“Yawaitar kai hare-haren da ake samu daga ɓangaren ƴan bindiga a cikin al’ummar gari akan kashe su tare da sace su matuƙar ana son a kawo karshen matsalar, sai an ƙara himma wajen samar da makamai ga jami’an tsaro tare da samar da sabbin dabaru domin kawar da matsalar, “in ji Galadanci”.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki kaɗan da sako ɗalibai aƙalla su sama da 285, na makarantar Kuriga dake ƙaramar hukumar Chikun ta jihar Kaduna, da ƴan bindiga suka sace su a baya, baya ga wasu ɗaliban da aka sace a wata makarantar Tsangaya a jihar ta Kaduna, wanda ko a jihar Borno ma aka jiyo yadda aka sace ƴan gudun hijira da dama a baya-bayan nan, inda matsalolin tsaron ke ƙara yin gaba a sassan ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Kano ya kafa kwamitin duba yadda ake rabon tallafin abincin Azumi

Published

on

Gwamnatin Kano ta kafa kwamitin duba yadda ake ciyarwar azumin watan Ramadan, a kananan hokumomin cikin birnin jihar 8, domin sa ido da duba yadda ake gudanar da aikin dafawa da rabawa al’umma abincin.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin ne ƙarƙashin kulawar mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da wasu ƴan kwamitin.

Hakan na zuwa ne dai bayan da gwamna Abba Kabir, ya ziyarci wasu daga cikin wuraren da ake dafa abincin, inda ya nuna rashin jin daɗin sa kan yadda ya ga aikin ke gudana a karamar hukumar kumbotso.

Bayanin hakan ya fito ne ta cikin wata sanarwar da babban mai taimakawa gwamnan Kano, na musamman akan gidajen rediyo Bashir Aminu Fanshekara, ya aikowa manema labarai, ya ce an bayyana Alhaji Danyaro Yakasai, a matsayin wanda zai jagoranci kwamitin mai mambobi 7.

Fanshekara ya ce kwamitin ya fara zagayawa wasu daga cikin mazaɓu dake karamar hukumar kumbotso, domin duba yadda ake dafawa da kuma raba abincin tallafin ga al’umma, inda suka suka fara da mazaɓar Na’ibawa a ranar Asabar 23 ga watan Maris ɗin shekarar 2024.

Continue Reading

Ilimi

Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.

 

An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.

 

Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.

 

“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.

 

Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.

Continue Reading

Trending