Connect with us

Labarai

Ministan lafiya zai kawo ziyara asibitin AKTH

Published

on

Ministan ma’aikatar lafiya ta tarayyar Nijeriya, Osagie Emmanuel Ehanire, zai kawo ziyarar jaje ga asibitin koyarwa na Mallam Aminu Kano wato AKTH, sakamakon ballewar cutar zazzabin Lassa da a ka samu a asibitin har ta yi sanadiyar rasa rayukan wasu likitoci guda biyu Dr Habibu Musa da Kaltum Abba da kuma Dr Abdulkadir Abubakar wanda ya rasa ransa ta sanadiyar hadarin mota.

Ministan zai dai kawo ziyara ne a gobe Asabar 25 ga watan da muke ciki domin jajantawa asibitin da kuma al’ummar jihar Kano dama gwamnati baki daya.

A cikin wata sanarwa wadda ta fito daga asibitin na AKTH, ta ce haka zalika wata cibiya ta lafiya da kimiyar kayayyakin aiki ta Nijeriya ta bada tallafin wata na’ura guda biyu ga asibitin wadda za ta ke kula da aukuwar yaduwar cututtuka a cikin asibitin.

Da yake bayar da tallafin na’urorin biyu, Alhaji Sani Abubakar, ya ce”na’urorin suna da matukar amfani kuma nan da nan suke bayyana alamar yanayin mutum nan take da zarar an sami wata cuta a jikin sa.

Ya kuma mika sakon ta’aziyar sa ga iyalan mamatan sannan ya kuma yi addu’ar samun lafiya ga wadanda a ke zargin cutar ta Lassa ta kama.

Da yake karbar na’urorin, shugaban asibitin na AKTH, Farfesa Abdurrahman Aabba Sheshe, ya godewa kamfanin bias wannan na’urar da ya baiwa asibitin gudunmawar sa sannan ya kuma tabbatar da cewa za a saka na’urorin a dakin bada kulawar gaggawa da hatsari da kuma dakin karbar haihuwa.

Sannan ya kuma bukaci al’umma da su daina yada jita-jita akan yaduwar cutar ta Lassa kamar yadda a ke kozanta ta kuma ya ce jita-jitar ta nuna cewa marasa lafiya sun daina ziyarta asibitin sakamakon barkewar cutar ta Lassa wanda hakan sam maganar bah aka ta ke ba.

 

Labarai

Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama

Published

on

Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.

Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.

Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.

Continue Reading

Labarai

Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam

Published

on

Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.

Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.

Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.

Continue Reading

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Trending