Connect with us

Manyan Labarai

Ana zargin Farfesa da satar yara

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta shirya gurfanar da Farfesa Solomon Musa Tarfa a gaban babbar kotun jiha sakamakon zargin satar yara da a ke yi masa.

Tun da farko dai gwamnatin na zargin Farfesa Solomon Tarfa da laifin satar kananun yara 19, wanda kunshin tuhumar zargin ya bayyana cewar, an gurfanar da Farfesa Solomon Musa Tarfa mazaunin unguwar Nomansland gida mai lamba 15 wanda a ka samu yara maza da mata  19 a cikin gidan sa kuma bincike ya nuna cewar sato yaran ya yi domin ya yi safarar su.

A kan hakan ne gwamnatin jihar ta gurfanar da shi a gaban babbar kotun jiha a ranar 13 ga wannan watan.

Lauyan gwamnati Lamido Abba Soron Dinki, shi ne ya baiwa Farfesa Tarfa, kunshin tuhumar shi kuma Farfesa ya sanya hannu a kai.

A baya dai kotun Majistret mai lamba 29 ta bayar da belin Farfesa Tarfa, sai dai an sanya sharuda a kan belin.

Sai  dai kuma, babban sakatare daga gwamnatin tarayya ya tsaya masa, amma dai lauyoyin sa sun garzaya gaban Justice Faruk Adamu Lawan na babbar kotun jiha mai lamba 7 domin ya sassauta wancan sharadin.

Koda yake lauyoyin gwamnati, Sanusi Ma’aji da Lamido Soron Dinki, sun yi suka sun roki kotun da ta juyar da rokon zuwa babbar kotun jiha mai lamba 2 wadda ita ce za ta saurari shari’ar.

Wakilin mu Yusuf Nadabo Ismail ya ruwaito cewar, an kawo Farfesa Solomon Tarfa cikin kotun Majistret mai lamba 29 sanye da sarka a kafar sa.

 

Manyan Labarai

Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokar gwajin lafiya kafin aure

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a kan dokar da za ta wajabta yin gwajin lafiya gabanin aure a faɗin jihar ta kano baki ɗaya.

A cikin wata sanarwa da ta samu sa hannu kuma ta fito daga ofishin babban daraktan yada labarai na gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa, ta ce an bijiro da dokar gwajin lafiya ne kafin aure, domin rage yawan yaran da ake haihuwa ɗauke da wasu cututtuka da ake iya ɗauka ko kuma gadonsu daga iyaye, kamar irin cutar Sikila da HIV da kuma ciwon hanta.

Rahotanni sun bayyana cewa, hakan na nufin cewa daga yanzu babu wani aure da za’a ɗaura a jihar har nan sai an gabatar da takardar sakamakon gwajin ƙwayoyin halittun gado, da na cutar hanta (Hepatitis B da C), da na ƙwayar cuta mai karya garkuwar jiki wato (HIV).

Gwamna Abba Kabir ya sanya hannu kan dokar ne, bayan kwashe mako guda da majalisar dokokin jihar ta amince da ita.

Sannan kuma dokar ta haramta tsangwamar mutane masu fama da cuta mai karya garkuwar jikin ɗan adam wato HIV, ko kuma cutar amosanin Jini Sikila, ko cutar Hanta, da sauran su.

Har ila yau, sanarwar ta ce dokar za ta fara aiki ne, daga ranar 13 ga watan Mayu na shekarar 2024 da ake ciki.

Continue Reading

Manyan Labarai

Lauya ya nemi a biya Abduljabbar Kabara Naira miliyan 20 saboda ɓata masa lokaci da aka yi.

Published

on

Babbar kotun jaha a ɓangaren ɗaukaka ƙara ƙarƙashin masu Shari’a Aisha Mahamud, da Nasir Saminu, sun sanya ranar 9 ga wannan watan da ake ciki dan ci gaba da sauraron daukaka karar, da Abduljabbar Nasir Kabara ya shigar.

A zaman kotun na yau lauyan Abduljabbar, Barrista Yusuf Sadik, ya shaidawa kotun cewar a shirye suke a fara sauraron daukaka karar.

Sai dai lauyan gwamnati ya bayyana cewar basu shirya ba dan haka a sanya wata ranar.

Lauyan Abduljabbar ya shaidawa kotun cewar sun bai wa lauyoyin gwamnati takardun bayaninsu tun a watan 2 da ya gabata, dan haka a biya Abduljabbarun Naira miliyan 20 saboda ɓata masa lokaci da aka yi.

Sai dai lauyan gwamnati ya yi suka an kuma duba lokacin da aka bada takardun a watan uku ne dan haka wannan lauya ya janye rokonsa.

Daga nan ne kotun ta sanya ranar 9 ga watan nan na Mayu da ake ciki, an kuma umarci lauyan gwamnati da ya yi martani idan yana da shi kafin wannnan rana.

Wakilinmu na Kotu Yusuf Nadabo Isma’il ya rawaito cewa, Abduljabbar Nasir Kabara dai ya daukaka karar ne dan kalubalantar hukuncin kutun shari’ar muslunci ta kofar kudu, wadda ta yanke masa hukuncin kisa ta hanya rataya bisa samunsa da laifin ɓatanci.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gobara ta ƙone tarin kayayyaki a gidan tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau

Published

on

Wata Gobara ta tashi a Gidan Tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau dake Mudubawa a yankin Karamar hukumar Nassarawa, inda ta ƙone wasu kayayyaki a ɗakin matar sa waɗanda zuwa yanzu ba’a ƙayyade ba.

Rahotanni sun bayyana cewa gobarar ta faro ne daga ɗakin Girki na matar tsohon gwamnan Hajiya Halima Shekarau, tun yammacin jiya Lahadi.

Da yake tabbatar da faruwar al’amarin, mai magana da yawun tsohon Gwamnan Malam Sule Ya’u Sule, ya ce gobarar ta shafi iya daki ɗaya ne a cikin gidan dake Munduɓawa.

A nasa ɓangaren kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano, PFS Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce da zarar sun kammala tattara alƙaluma da bincike, zai magantu a nan gaba.

Continue Reading

Trending