Connect with us

Labarai

Covid-19: Gwamnati ta kara kaimi wajen yaki da Corona -SEDSAC

Published

on

Kungiyar bunkasa ilimi da al’amuran jama’a da demokradiyya SEDSAC, ta al’umma na da rawar da za su taka wajen dakile yaduwar cutar Coronavirus a cikin zamantakewar al’umma wajen kulawa da yaduwar cutar ta hanyar rage cinkoso.

Cikin wata sanarwa mai kunshe da sa hannun babban daraktan kungiyar, Kwamrade Hamisu Kofar Na’isa, ya sanyawa hannu a ka kuma rabawa manema labarai, kungiyar ta ce kamata ya yi gwamnati ta sa dokar ta bace wajen hana zirga-zirgar ababan hawa a dukannin titinan jihohin kasar nan baki daya domin gudun yada cutar a cikin jihohin Nijeriya.

Sanarwa ta kuma ce gwamnati da ta kara tsaurara matakan kariya sosai domin yakar cutar Covid-19 domin kuwa cutar ta na da matukar hadari ga rayuwar al’ummar Nijeriya da ma duniya baki daya.

Sannan ta kuma bukaci al’umma da su ci gaba da bin umarnin jami’an lafiya da kuma shawarwarin su, gudun kamuwa da cutar ta Covid-19 tare da bin duk wasu hanyoyi da za a magance yafuwar cutar domin kare lafiya baki daya.

Haka zalika, ta kuma ce tabbas wannan cuta ta Covid-19 ta kawo tasgaro a fannin a fannin da sauran al’amura, domin haka kamata ya yi gwamnati ta dauki matakin gaggawa domin farfado da fannin ilimi da sauran al’amura baki daya.

Sannan ta kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta jiha da ta rage kudaden gudanar da manyan ayyukan gwamnati na wannan shekarar sakamakon farashin man fetur da ya yi kasa domin al’umma su amfana. Sakamakon cewa halin da a ke ciki na wajen tattalin arizki Nijeriya ta dogara da man fetur domin haka rage farashin man ba zai shafi tattalin arikin kasar nan ba.

Labarai

Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama

Published

on

Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.

Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.

Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.

Continue Reading

Labarai

Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam

Published

on

Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.

Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.

Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.

Continue Reading

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Trending