Connect with us

Labarai

Binne gawa: Matashi ya dauke wa mutum waya a makabarta

Published

on

A na zargin wani matashi mai suna Abdullahi Idris Sudawa mai shekaru 40, da satar waya a na tsaka da binne gawa a makabartar Abbatuwa da ke Kofar Mazugal.

Matashin dai al’ummar da su ka zo binne gawar sun yi nasarar kama shi ne bayan ya yanka aljihun wani mutum ya na yunkurin satar wayar lokacin da a ke binne gawa.

Gidan radiyon Dala ya zantawa da Abdullahi Idris inda ya bayyana yadda al’amarin ya faru.

Ya ce, “Waya ce na dauka kuma na bai wa mai ita kayar sa, a cikin makabarta ne abun ya faru, ban san mai ita ba, amma kuma na ba shi kayan shi, ba ‘yan unguwar mu ba ne, tsayawa na yi addu’a… Gaskiya na fada na dauka na kuma bayar, ban san kudin wayar ba, kuma da yardar Allah na yi na farko na yi na karshe, idan na sata a kwai wanda na ke kai wa a Wapa ya siya… Kauyuka na ke zuwa yin sata, idan mutum ya na tafiya in saka masa hannu a aljihun gefe”. A cewar Abdullahi Idris

Suma dai wasu daga cikin wadanda su ka halarci binne gawar kuma abun ya faru a kan idanunsu sun yi mana karin bayani.

“Sunana Zahradden Shu’aibu Haruna. Mun je makabartar Abbatuwa mun ajiye baburan mu mun shiga ciki sai a ka kama wasu sun yanka aljihun mutane su na kokarin daukar mu su wayoyi, sai mu ka fito fito waje, na zo zan dauki babur di na na gan shi a bude, abun ya razana ni, wannan abun ya zama ruwan dare, a dauke wa mutane abun hawa”.

“Sunana Isah Rabi’u Ahmad Goran dutse. Daya daga cikin wadanda su ka kama gawa za’a saka a kabari wayar sa ta fada cikin kabari ya zaro wayar ya miko a rike masa, a wajen ba’a san wanda ya karbi wayar ba saboda rashin imani na al’umma, sannan a ka samu mutane an yanka masu aljihu, mu ka fito mu ka ga an bude kan baburan mu”. A cewar ganau

Shugaban ‘yan bijilante na yankin Kofar Mazugal, Danlami Kwamanda ya ce, “Abun ya ba ni mamaki, rashin tsoron Allah irin na mutane, a cikin makabarta an zo sa gawa, amma barayi su zo suna sata a makabarta, ka duba yadda kan babura su ke a bude, barawon nan ba shi kadai ba ne”. Inji Danlami Kwamanda

Wakilin mu Abubakar Sabo ya rawaito cewar, Danlami Kwamanda ya kuma ce, yanzu matakin da za su dauka sai sun ga karshen wannan abun, domin za su kai shi ga hukuma a dauki matakin.

Labarai

Abin takaici ne yadda ake fuskantar ƙarancin ruwan Sha a sassan jahar mu – Gwamnan Kano.

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya nuna rashin jin daɗin sa bisa yadda ake samun ƙarancin Ruwan Sha, a wasu daga cikin sassa jihar Kano.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga manema labarai, a lokacin a ya kai ziyarar gani da ido, matatar Ruwa da ke Tamburawa a yammacin yau Juma’a, a ƙokarin sa na na gyara ɓangaren ruwan a cikin garin Kano.

Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma sha alwashin tabbatar wa al’umma cewar, gwamnatin sa za ta yi aiki ba dare ba rana domin tabbatar da isasshen ruwan Sha ga al’ummar jihar Kano.

Gwamnan ya ƙara da ce a lokacin da suka zo ba sufi mako biyu ba suka samar da ingantaccen Ruwan sha, wanda ya rinƙa shiga cikin lunguna da Sako na sassan jihar.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da sayar da Burtalai a wasu garuruwan ta

Published

on

Biyo bayan kokawar da wasu Fulani Makiyaya suka yi kan yadda wasu suka gididdiba burtalai yayin da aka siyarwa Manoma, a garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, yanzu haka ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da taɓawa, ko kuma sayar da dukkanin Burtalan kiwon shanun ba tare da ɓata lokaci ba.

Shugaban riƙon ƙaramar hukumar ta Tofa Abubakar Sulaiman Mai Rogo, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a ranar Alhamis.

Mai Rogo, ya kuma ce ƙaramar hukumar ba ta da hannu a kan taɓa dukkan guraren, a dan haka sun dakatar da dukkanin yunƙurin taɓa Burtalan har sai shugabanni na kwamitin ƙasa sun kammala bincike wanda yanzu haka ake ci gaba da yi.

Da yake nuna jin daɗin sa kan matakin dakatarwar, amadadin Fulanin garuruwan, shugaban ƙingiyar Funali Makiyaya ta Gan Allah, Ahmad Shehu Gajida, yabawa gwamnatin jihar Kano, da kuma ƙaramar hukumar ta Tofa ya yi, bisa karɓar koken su da suka akai.

A baya-bayan nan ne dai a zantawar Dala FM Kano, da wasu Funalani Makiyaya mazauna garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, suka koka kan yadda aka gididdiba burtalan a yankunan nasu aka siyarwa manema, lamarin da suka ce ka iya sawa su rasa guraren da za suyi kiwon shanun su wanda hakan babbar barazana ce a gare su.

Continue Reading

Labarai

Ku guji zubar da Shara barkatai a muhallan ku – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta gargadi al’umma da su kaucewa zubar da shara a wuraren da ba’a tanade su ba, domin kaucewa yawaitar samun cutuka a tsakanin al’umma, duba da yadda ake ci gaba da tunkarar lokacin Damuna.

Shugaban hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar Kano Ambasada Ahmadu Haruna Zago, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake sanya ido kan aikin kwashe sharar da ke unguwar Zango hauran gadagi bayan Festival.

Ya ce duba da yadda Damuna ke ci gaba da tunkarowa, akwai bukatar al’umma su fahimci cewa zubar da shara barkatai ka iya haifar da cututtuka daban-daban ga iyalan su, musamman ma kasancewar sharar da ke unguwar ta Zango bayan Festival, tana tsakiyar gidajen al’umma ne da kasuwa da kuma makaranta.

Nazifi Mohammed Usman mai Duniya, da Mohammed Ibrahim wato Halifa mai Gas mazauna unguwar ta Zango ne, sun ce tarin sharar a cikin unguwar su babban ƙalubale ne a gare su, domin kuwa taruwar da tayi har ta kan shiga cikin makarantar yankin su.

Shugaban hukumar kwashe sharar Ahmadu Zago, ya kuma sha alwashin yin duk mai yiwuwa wajen tsafta ce birnin Kano, wajen kwashe shara daga kowane yankin, domin gudun faruwar ambaliyar ruwa sanadin sharar da ka toshe magunan ruwa a jihar Kano.

Continue Reading

Trending