Addini
Ganduje ya kaddamar da ma’aikatar kula da al’amuran addinai

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ƙaddamar da ma’aikatar lura da al’amuran addinai a gidan Murtala da ke Kano a ranar Litini.
Ya ce, “Ma’aikatar za ta riƙa kula da hukumomin da ke kula da harkokin addinin musulunci da kuma ɓangaren musuluntar da maguzawa tare da inganta mu’amala tsakanin musulmi da waɗanda ba musulmi ba domin samun zaman lafiya”.
Ya kuma ce, “Ma’aikatar za ta riƙa shirya kasafin kuɗin da za ta kashe a duk shekara, kuma mu na kira ga ma’aikatan da ke ƙarƙashin ma’aikatar da su ci gaba da bada haɗin kai wajen tafiyar da ayyukan ma’aikatar yadda ya kamata”. A cewar Ganduje
Da yake jawabi a yayin ƙaddamar da ma’aikatar kwamishinan addinai na Kano, Muhammad Tahar Adam ya ce, “Wannan rana ce mai tarihi, kasancewar ba a taɓa samun ma’aikatar da gwamna ya je bude ta da kan sa ba sai wannan”. Inji Muhammad Tahar Baba Impossible
Wakiliyar mu Zahra’u Nasir ta rawaito cewar, kwamishinan ya kuma ce, yanzu haka shekarar ma’aikatar guda da fara aiki, kuma za ta ɗora da ayyukan ta wajen tabbatar da ci gaban addinin musulunci a jihar Kano.

Addini
Hukumar Shari’a ta shirya buɗe baki ga Mutanen da suka musulunta a Kano

A ƙoƙarin ta na ƙara ɗaɓɓaƙa harkokin addinin Musulunci, hukumar Shari’ah ta jihar Kano da haɗin guiwar kungiyar World Assembly of Muslim Youth (Wamy), sun shirya wa waɗanda suka karbi addinin Musulunci shan ruwa a ranar Lahadi 23 ga Ramadan shekarar 1446.
Taron shan ruwan dai ya gudana ne a harabar hukumar karkashin Jagorancin Mukaddashin Shugaban ta Sheikh Ali Ɗan Abba.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Muƙaddashin Daraktan yaɗa labarai na hukumar shari’a ta jihar Kano, Musa A Ibrahim (Best Seller).
Hukumar Shari’ar ta kuma ayyana ranar 15 ga Ramadan domin ta zama ranar da za ta rinƙa shan ruwa da waɗanda suka karɓi addinin Musulunci da za a rinƙa yi a duk shekara.
“Muna kuma miƙa godiya ga gwamnatin jihar Kano a karkashin gwamna Abba Kabir Yusuf, da ƙungiyar World Assembly of Muslim Youth [WAMY] da suka ba mu gudummawa wajen shirya wannan taron, “in ji Sheikh Ali”.
Taron shan ruwan dai ya sami halartar dukkanin shugabannin hukumar da mambobin ta da kuma ma’aikatanta tare da shugabannin kungiyar WAMY, da wasu manyan mutane da suka halarta.
Da yake nasa jawabin wakilin shugaban kungiyar Wamy Alhaji Sanusi, ya nuna jin daɗinsa da yadda wannan shan ruwa ya gudana, kuma ya tabbatar da cewar kungiyar su ƙungiya ce ta taimakon addinin musulunci da musulmi a ko ina suke, kuma kungiyar zata ci gaba da wannan aikin alherin da izinin Allah S.W.T.

Addini
Ku taimakawa mabuƙata da Naman Sallah bisa halin matsin rayuwar da ake ciki – Limami

Babban limamin masallacin juma’a na Alaramma Abubakar Ɗan Tsakuwa, da ke unguwar Ja’en Ring road Mallam Abdulkareem Aliyu, ya yi kira ga al’ummar Musulmi, da su kiyaye ƙa’idojin yanka Dabbobin Layyah, domin gujewa cin mushen Nama.
Mallam Abdulkareem Aliyu, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u, lokacin da yake tsokacin huɗubar da ya gabatar ranar Sallar Idin da ya jagoranta a masallacin ranar Lahadi 17 ga watan Yunin 2024.
Ya ce a mafi yawan lokuta al’umma sukan yanka dabbobi amma rashin bin ƙa’idojin yanka yakan sanya wa su ci mushen nama ba tare da sun sani ba, a dan haka su tashi tsaye wajen sanin yadda ake yanka Dabbobin a mahanga ta addinin Musulunci.
A cewar sa, “Musulmai ku kwaɗaitu da yin sadakar naman layya musamman ma ga masu ƙaramin ƙarfi domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T, “in ji shi”.
Mallam Abdulkareem Aliyu, ya kuma ce, akwai buƙatar a kiyaye nau’ikan dabbobin da aka sahale ayi layya da su, waɗanda suka haɗar da nau’in Sa ko Saniya, da kuma Raƙumi ko Raƙuma (Taguwar), ko kuma Rago ko Tinkiya, ko Akuya ko kuma Ɗan Akuya.
Wannan dai na zuwa ne bayan da al’ummar Musulmin Duniya suka gudanar da babbar Sallah, a jiya Lahadi 16 ga watan Yunin shekarar 2024.

Addini
An ga jinjirin watan Zul-Hijjah a Najeriya, ranar Lahadi 16 ga watan Yuni Babbar Sallah

Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Abubakar Sa’ad na uku, ta sanar da ganin jinjirin watan Zul-Hijjah na shekarar 1445.
Hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta fitar, mai ɗauke da sa hannun Wazirin Sakkwato, kuma shugaban kwamitin duban wata Farfesa Sambo Wali Junaid.
Sanarwar ta kuma ce duba da ganin jaririn watan na Zul-Hijjah da akayi a jiya Alhamis, hakan ya tabbatar da cewar yau Juma’a ɗaya ga watan Zul-Hijjah, wanda za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan Yunin 2024.
Tun dai a jiya Alhamis hukumomi a ƙasar Saudiyya suka sanar da ganin Jaririn watan na Zul-Hijjah, lamarin da ya kasance za’ayi tsayuwar Arafa a ranar Asabar 15 ga watan Yunin 2024, yayin da za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan na Yuni.
Kafar Dala FM Kano, ta rawaito cewa, kawo yanzu dai maniyyata aikin hajjin bana da dama ne ke ci gaba da shiga ƙasa mai tsarki, a ƙoƙarin su na zuwa domin sauke Farali.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su