Connect with us

Labarai

Kotu na tuhumar matashi da bata sunan budurwa a Facebook

Published

on

Kotun majistret mai lamba 86 karkashin mai shari’a Faruk Ibrahim Umar ta sanya wani matshi a hannun beli.

Matashin mai suna Abubakar Muhammad a na zargin shi da laifin bata suna ta hanyar sanya hoton wata budurwa Aisha Ibrahim Babaji, ya hada ta da hotunan batsa ya na yadawa a dandalin sada zumunta na Facebook.

Yayin da a ka karanta tuhumar ya musanta zargin lauyan sa ya roki kotun da ta bayar da belin sa.

Mai shari’a Faruk Ibrahim Umar ya amince da rokon, sai dai ya ayyana cewar, sai an gabatar da mutum 2 masu kima kuma wadanda su ke da gida a karkashin hurumin kotun idan kuma ya tsere za su biya miliyan daya kowannen su.

A zantawar wakilin mu da lauyan mai kara Barista Husaini Ahmad Makari ya ce, “A na zargin Abubakar Muhammad ne da yada hoton batanci ga Aisha Babaji yayin da ya ke yanke fuskar ta yada hotunan tsiraici har ma da kawayen ta da su ka saka baki, bayan bincike a ka gano shi kuma a ka gurfanar da shi a gaban kotu”.

Itama Aishar ta bayyana yanda ta ji lokacin da hotunan ta suke yawo a Facebook tare da hotunan batsa.

Ta na mai cewa, “Mun hadu da shi ne a wajen aiki sai ya nuna ya na so na har ya ce zai turo nan bada dadewa ba, sai na ce ya yi hakuri sai nan gaba, shi ne ya dauki hotuna na ya na hadawa ya turawa kawaye na da ‘yan uwa na, ni yanzu ina so a bi min hakki na”. A cewar Aisha Babaji.

Lauyan da ya ke kare matashin, Barista Aliyu Umar Faruk ya bayyana matsayar su a kan batun inda ya ce, “Na farko dai tuhuma ce kamar yadda ‘yan sanda su ka saba yi, amma har yanzu a idon shari’a shi ba mai laifi ba ne, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya nuna, saboda haka kotu ce kawai za ta iya tabbatar da mai laifi ne ko ba mai laifi ba ne”.

Wakilin mu Yusuf Nadabo Isma’il ya rawaito cewa, Kotun ta sanya ranar 8 da 9 ga wata domin fara sauraron shaidu.

 

 

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Labarai

Dilolin Wiwi sun yanki mai unguwa da Wuƙa, tare da cizon shi a hannu, kan ya shana su sha da siyar da wiwi a Kano

Published

on

Wasu matasa da ake zargin ƴan Daba ne, kuma dilolin Wiwi, sun kai wa mai unguwar yankin Bachirawar Tukwane ƙarshen kwalta hari da muggan makamai.

Tun farko dai mai unguwar yankin Malam Mustapha ya shawarci matasan ne, da su dai na ɗaurin tabar Wiwi, da siyar wa a kofar gidajen mutane lamarin da ya tunzura matasan.

Matasan dai sun rutsa mai unguwar Bachirawar ne inda suka yi yunƙurin hallaka shi, bayan da suka yanke shi da Wuƙa, tare da cizon sa a Hannu, sai dai ‘yan ƙungiyar bijilante na yankin sun kawo masa ɗauki inda suka kama wani matashi mai laƙabin Kokuwa.

A lokacin ne kuma mutanen yankin suka yi yunƙurin ɗaukar doka a hannu, sai dai mai unguwar Bachirawa Malam Mustapha dan Bachirawa Gabas Malam Abdulkadir Dandiyo, sun kuɓutar da matashin inda aka mika shi ofishin ƴan sanda, ragowar matasan suka tsere.

Shugaban kungiyar ci gaban al’ummar yankin Dakta Jibrin Sagir, ya ce a shirye suke su tinkari duk wani ɓata gari a yankin da yake addabar su.

Continue Reading

Trending