Connect with us

Labarai

Kotu na tuhumar matashi da bata sunan budurwa a Facebook

Published

on

Kotun majistret mai lamba 86 karkashin mai shari’a Faruk Ibrahim Umar ta sanya wani matshi a hannun beli.

Matashin mai suna Abubakar Muhammad a na zargin shi da laifin bata suna ta hanyar sanya hoton wata budurwa Aisha Ibrahim Babaji, ya hada ta da hotunan batsa ya na yadawa a dandalin sada zumunta na Facebook.

Yayin da a ka karanta tuhumar ya musanta zargin lauyan sa ya roki kotun da ta bayar da belin sa.

Mai shari’a Faruk Ibrahim Umar ya amince da rokon, sai dai ya ayyana cewar, sai an gabatar da mutum 2 masu kima kuma wadanda su ke da gida a karkashin hurumin kotun idan kuma ya tsere za su biya miliyan daya kowannen su.

A zantawar wakilin mu da lauyan mai kara Barista Husaini Ahmad Makari ya ce, “A na zargin Abubakar Muhammad ne da yada hoton batanci ga Aisha Babaji yayin da ya ke yanke fuskar ta yada hotunan tsiraici har ma da kawayen ta da su ka saka baki, bayan bincike a ka gano shi kuma a ka gurfanar da shi a gaban kotu”.

Itama Aishar ta bayyana yanda ta ji lokacin da hotunan ta suke yawo a Facebook tare da hotunan batsa.

Ta na mai cewa, “Mun hadu da shi ne a wajen aiki sai ya nuna ya na so na har ya ce zai turo nan bada dadewa ba, sai na ce ya yi hakuri sai nan gaba, shi ne ya dauki hotuna na ya na hadawa ya turawa kawaye na da ‘yan uwa na, ni yanzu ina so a bi min hakki na”. A cewar Aisha Babaji.

Lauyan da ya ke kare matashin, Barista Aliyu Umar Faruk ya bayyana matsayar su a kan batun inda ya ce, “Na farko dai tuhuma ce kamar yadda ‘yan sanda su ka saba yi, amma har yanzu a idon shari’a shi ba mai laifi ba ne, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya nuna, saboda haka kotu ce kawai za ta iya tabbatar da mai laifi ne ko ba mai laifi ba ne”.

Wakilin mu Yusuf Nadabo Isma’il ya rawaito cewa, Kotun ta sanya ranar 8 da 9 ga wata domin fara sauraron shaidu.

 

 

Hangen Dala

Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Hangen Dala

Rashin wuta:- Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

 

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

 

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

 

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

 

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

 

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

 

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Labarai

Ci gaba ba ya zuwa sai an samu haɗin kan al’umma – Dagacin Ja’en

Published

on

Dagacin garin Ja’en da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano, Alhaji Isma’il Sa’ad Usman, ya ce hadin kai ne kaɗai zai kawo ci gaba ga kowa ce irin al’umma.

Dagacin ya bayyana hakan ne Jim kaɗan bayan wani taron masu Ruwa da tsaki na Garin Ja’en, wanda Hakimin Gundumar Ɗorayi Barde Kerarriya Alhaji Shehu Kabir Bayero ya shirya, aka gudanar a yankin Ja’en a ƙarshen makon da ya gabata.

“Dukkanin wani ci gaba ba ya zuwa har sai an samu haɗin kan kowa ne bangare na al’umma, “in ji Dagacin”.

Wakilin Dala FM Kano, Ahmad Rabi’u Ja’en ya ruwaito cewa, taron ya samu halartar dukkanin bangarori, na unguwannin Ja’en, da suka haɗar da kungiyar mafarauta da maharba dabma kungiyar malaman makaranta.

Continue Reading

Trending