Connect with us

Labarai

Babu wanda ya cancanci shan romon dumukradiya sai talaka – Farfesa Kamilu Fagge

Published

on

Masanin kimiyyar siyasa a Jami’ar Bayero da ke jihar Kano Farfesa Kamilu Sani Fagge, ya ce, babu wanda ya cancanci ya sha romon dumukradiya kamar talaka, duba da su ke jefawa shugabanni kuri’a har su samu su dare kujerar mulki.

Farfesa Kamilu Sani Fagge, ya bayyana hakan ne a zantawar sa da gidan rediyon Dala a ranar Alhamis

Haka zalika, shima wani masanin tattalin arziki a Jami’ar Yusuf Maitama sule da ke jihar Kano Dr. Yusuf Ibrahim Kofar Mata ya ce, “Idan har gwamnatin kasar nan na san shawo kan matsalar halin matsin rayuwa da a ke ciki, babu shakka sai ta tuntubi shawararin masana kan harkokin tattalin arzikin”. Inji Dakta Yusuf Ibrahim Kofar Mata

Wakiliyar mu Shamsiyya Farouk Bello ta rawaito cewa, a yayin da Najeriya za ta cika shekarun 60 da samun ‘yan cin kai a tafarkin dumukradiya, amma masana na ganin har dan Najeriya bai ci ribar dumukradiyar ba.

 

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending