Connect with us

Labarai

#EndSARS: An fara horas da sabuwar rundunar ƴan sanda ta SWAT

Published

on

A yau Litinin ne za a fara horas da jami’an sabuwar rundunar ƴan sanda ta SWAT da zata maye gurbin rundunar SARS da aka soke.

Rundunar ƴan sanda dai ta ce, jami’an da aka zaɓa waɗanda za su kasance cikin sabuwar rundunar matasa ne masu jini a jika kuma dukkansu sun shafe aƙalla shekara bakwai suna aikin ɗan sanda.

Sannan jami’an ba su da wani tabo ko kuma tarihi na laifi da suka aikata a baya, ba a kuma taɓa samunsu da laifin take haƙƙin bil adama ba ko kuma saɓa ƙa’idar amfani da makami.

Za dai a soma horas da ‘yan sandan ne a kwalejojin horas da ‘yan sanda na Ila Oragun, da ke jihar Osun da kuma kwalejin horas da ‘yan sanda ta jihar Nasarawa.

To sai dai masana tsaro na cewa da sauran aiki a gaban rundunar ƴan sanda matuƙar ba ta nazarci sake inganta ayyukan jami’anta ba maimakon sabuntawa, a cewar mai sharhi kan tsaro Malam Mustapha Isyaku da ke digirinsa na uku kan tsaro a makarantar sojoji ta NDA da ke Kaduna.

“Ni ina ganin abin da ya fi mahimmanci ba wai yau a ce an soke SARS sannan ayi hanzari a kirkiri SWAT ba, saboda babu wani dan Najeriya da ya ke ganin su SWAT ba za su yi abinda su SARS su ka yi ba” a cewarsa.

Ya kara da cewa “Ina ganin abin da ya fi mahimmanci shi ne a mayar da hankali wajen inganta gabaki daya tsarin rundunar ‘yan sanda, ya kasance kafin ma a dauki mutum ‘dan sanda an tantanceshi, ya kuma wuce duk wasu ka’idoji da horo da ya kamata a ce ya samu”

Ya ci gaba da cewa “Sannan akwai bukatar ci gaba da horas da su lokaci bayan lokaci, sannan akwai bukatar  samar musu da kayayyakin aiki na zamani, sannan a koyar dasu gyara alaka tsakaninsu da al’umma, idan ba a yi haka ba babu wani sauyi da za a samu”.

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Labarai

Dilolin Wiwi sun yanki mai unguwa da Wuƙa, tare da cizon shi a hannu, kan ya shana su sha da siyar da wiwi a Kano

Published

on

Wasu matasa da ake zargin ƴan Daba ne, kuma dilolin Wiwi, sun kai wa mai unguwar yankin Bachirawar Tukwane ƙarshen kwalta hari da muggan makamai.

Tun farko dai mai unguwar yankin Malam Mustapha ya shawarci matasan ne, da su dai na ɗaurin tabar Wiwi, da siyar wa a kofar gidajen mutane lamarin da ya tunzura matasan.

Matasan dai sun rutsa mai unguwar Bachirawar ne inda suka yi yunƙurin hallaka shi, bayan da suka yanke shi da Wuƙa, tare da cizon sa a Hannu, sai dai ‘yan ƙungiyar bijilante na yankin sun kawo masa ɗauki inda suka kama wani matashi mai laƙabin Kokuwa.

A lokacin ne kuma mutanen yankin suka yi yunƙurin ɗaukar doka a hannu, sai dai mai unguwar Bachirawa Malam Mustapha dan Bachirawa Gabas Malam Abdulkadir Dandiyo, sun kuɓutar da matashin inda aka mika shi ofishin ƴan sanda, ragowar matasan suka tsere.

Shugaban kungiyar ci gaban al’ummar yankin Dakta Jibrin Sagir, ya ce a shirye suke su tinkari duk wani ɓata gari a yankin da yake addabar su.

Continue Reading

Trending