Labarai
#EndSARS: Jihohi biyar aka sanyawa dokar hana fita a Najeriya

Jihar Ekiti da ke kudu maso yamma, da kuma Filato da ke tsakiyar arewacin Najeriya ne na baya-bayan nan da suka sanya dokar hana zirga-zirga na tsawon sa’o’i 24 a ranar Talata, bayan an tashi da dokar ta bacin a jihar Lagos.
JIHAR EDO
Jihar Edo ce daga Kudu-maso-Kudu ta fara sanya dokar ta baci, bayan balle gidan yari a Benin da ake zargin masu zanga-zangar sun yi a ranar Litinin.
Gwamnatin Edo ta sanya dokar hana fita har sai abin da hali ya yi, kuma dokar ta soma aiki ne nan take.
Gwamnan jihar, Godwin Nogheghase Obaseki, ya ce matakin sanya dokar ya zama dole ganin yadda fusatattun masu zanga-zangar ke kai hare-hare kan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba da sunan zanga-zangar EndSARS.

Yadda aka yi zanga-zanga a Edo
JIHAR LEGAS
A ranar 20 ga watan Oktoban 2020 ne, gwamnan Babajide Sanwo-Olu, ya ayyana dokar hana fita, wadda ta soma aiki da yammacin ranar Talatar.
Amma daga bisani aka sassauta dokar domin bai wa mutanen da suka fita aiki ko kuma wurin sana’a damar komawa gida, kafin dokar ta koma yadda take a baya.
Wannan ya zo ne sakamakon sauya salo da masu zanga-zangar #EndSARS suka yi na tayar da rikici, kamar yadda gwamnan ya bayyana.
Ko da yake gwamna, Sanwo-Olu, ya ce ma’aikatan da ya zama wajibi su fita aiki aka amince a gani a waje.
Amma duk da haka masu zanga-zangar sun bijirewa umarnin gwamnati, inda suka cigaba daga inda suka tsaya, lamarin da ya sanya sojoji suka isa wurin da ake zanga-zangar.

Yadda masu zanga-zanga su ka yi fitar dango a Legas da ke kudancin Najeriya
JIHAR FILATO
Gwamna, Simon Lalong, shima ya sanya dokar hana fita a Kudanci da kuma wasu kananan hukumomi da ke arewacin Jos wadda ta soma aiki daga karfe 8 na daren ranar Talata.
A wata sanarwa da ya fitar, gwamnan ya ce zanga-zangar da aka fara ta cikin wasu ‘yan kwanaki da suka wuce ta sauya zuwa rikici, bayan da aka samu bata gari suna amfani da zanga-zangar wajen kai hari da kuma cin zarafin jama’a.
An samu mutane cikin masu zanga-zangar da ke ta’adi da kone-konen motoci da farfasa shaguna a titin Ahmadu Bello da kona wani wajen ibada da ke titin Gyero a yankin Bukuru. Sannan akwai mutane 3 da suka mutu. In ji sanarwar

Gwamna Simon Lalong na jihar Filato
JIHAR ABIA
Gwamna Abia Okezie Ikpeazu, shima ya sanya dokar hana fita ta ba dare ba rana a Aba da Umuahia daga karfe 6 na yamma har sai abin da hali ya yi, a wani mataki na kare dukiyoyi da rayukan jama’a.
Wata sanarwa da gwamnan ya fitar ta hannun kwamishinan yada labarai, John Okiyi Kalu, ya ce ‘yan daba sama da 30 ne suka kaiwa wani ginin ‘yan sanda hari a lokacin zanga-zangar.

Masu zanga-zanga a jihar Abia kenan
Sanarwar ta tabbatar da cewa jami’in dan sanda guda ne ya rasa ransa sakamakon harin ‘yan dabar da ke dauke da makamai, inda suka kwace bindigogi da harsashai.
Ko da yake gwamnatin Abia ta ce an cafke mutum guda daga cikin maharan, sakamakon raunin da ya samu daga harbin bindiga.
JIHAR EKITI
Shima dai gwamna, Kayode Fayemi ya bayar da umarnin sanya dokar hana fita, bayan da bata gari suka sauyawa zanga-zangar EndSARS suna zuwa rikici.
Gwamnatin dai ta ayyana dokar hana fita ba dare-ba-rana, wadda ta shafi kowanni bangare a ranar Talata.

Yadda masu zanga-zanga suka fara fitowa a jihar Ekiti
Gwamnan ya bayyana damuwa kan yadda gangamin #EndSARS da aka soma a cikin lumana ya ya ke neman munana a jihar.
Wanne mataki gwamnatin Najeriya ta dauka?
Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya, Muhammad Adamu, ya bayar da umarnin a baza jami’an ‘yan sandan kwantar da tarzoma a sassan kasar, a wani bangare na shirin ko-ta-kwana.
Sanarwar babban sufeton ‘yan sandan, na zuwa ne bayan samun karuwar tashe-tashen hankula a wasu jihohi sakamakon zanga-zangar neman a rushe rundunar SARS ko kuma SWAT, bayan da aka zargi jami’an sashen da cin zarafin jama’a.

Labarai
Matashin da ke Sansana bayan Akuya yana sakawa a TikTok ya shiga hannun hukumar Hisbah a Kano

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wani Matashi da aka yi zargin ya sansana bayan wata Akuya, a matsayin yana son ya yi suna a shafukan sada zumunta.
Mataimakin babban kwamandan hukumar Hisbah Dakta Mujahideen Aminudeen Abubakar, ya shaidawa Dala FM Kano cewar, sun kama matashin ne mai suna Shamsu Yakubu dan garin Dawakin kudu, mai shekaru 24, bayan da dagacin garinsu ya kawo korafi akansa.
Dagacin ya ce an kai ƙorafin matashin ne saboda yadda mutanen garin suka yi kokarin farmasa, bayan da aka gano bidiyonsa a shafin TikTok yana sansana bayan Akuya.
Yanzu haka hukumar ta ɗauki matakin kai matashin a fara yi masa gwajin Ƙwaƙwalwa, da kuma na ta’ammali da kayan maye.

Labarai
Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.
Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.
Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.
Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.
A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Labarai
Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.
Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.
“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.
Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.
Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su