Labarai
#EndSARS: Jihohi biyar aka sanyawa dokar hana fita a Najeriya
Jihar Ekiti da ke kudu maso yamma, da kuma Filato da ke tsakiyar arewacin Najeriya ne na baya-bayan nan da suka sanya dokar hana zirga-zirga na tsawon sa’o’i 24 a ranar Talata, bayan an tashi da dokar ta bacin a jihar Lagos.
JIHAR EDO
Jihar Edo ce daga Kudu-maso-Kudu ta fara sanya dokar ta baci, bayan balle gidan yari a Benin da ake zargin masu zanga-zangar sun yi a ranar Litinin.
Gwamnatin Edo ta sanya dokar hana fita har sai abin da hali ya yi, kuma dokar ta soma aiki ne nan take.
Gwamnan jihar, Godwin Nogheghase Obaseki, ya ce matakin sanya dokar ya zama dole ganin yadda fusatattun masu zanga-zangar ke kai hare-hare kan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba da sunan zanga-zangar EndSARS.
JIHAR LEGAS
A ranar 20 ga watan Oktoban 2020 ne, gwamnan Babajide Sanwo-Olu, ya ayyana dokar hana fita, wadda ta soma aiki da yammacin ranar Talatar.
Amma daga bisani aka sassauta dokar domin bai wa mutanen da suka fita aiki ko kuma wurin sana’a damar komawa gida, kafin dokar ta koma yadda take a baya.
Wannan ya zo ne sakamakon sauya salo da masu zanga-zangar #EndSARS suka yi na tayar da rikici, kamar yadda gwamnan ya bayyana.
Ko da yake gwamna, Sanwo-Olu, ya ce ma’aikatan da ya zama wajibi su fita aiki aka amince a gani a waje.
Amma duk da haka masu zanga-zangar sun bijirewa umarnin gwamnati, inda suka cigaba daga inda suka tsaya, lamarin da ya sanya sojoji suka isa wurin da ake zanga-zangar.
JIHAR FILATO
Gwamna, Simon Lalong, shima ya sanya dokar hana fita a Kudanci da kuma wasu kananan hukumomi da ke arewacin Jos wadda ta soma aiki daga karfe 8 na daren ranar Talata.
A wata sanarwa da ya fitar, gwamnan ya ce zanga-zangar da aka fara ta cikin wasu ‘yan kwanaki da suka wuce ta sauya zuwa rikici, bayan da aka samu bata gari suna amfani da zanga-zangar wajen kai hari da kuma cin zarafin jama’a.
An samu mutane cikin masu zanga-zangar da ke ta’adi da kone-konen motoci da farfasa shaguna a titin Ahmadu Bello da kona wani wajen ibada da ke titin Gyero a yankin Bukuru. Sannan akwai mutane 3 da suka mutu. In ji sanarwar
JIHAR ABIA
Gwamna Abia Okezie Ikpeazu, shima ya sanya dokar hana fita ta ba dare ba rana a Aba da Umuahia daga karfe 6 na yamma har sai abin da hali ya yi, a wani mataki na kare dukiyoyi da rayukan jama’a.
Wata sanarwa da gwamnan ya fitar ta hannun kwamishinan yada labarai, John Okiyi Kalu, ya ce ‘yan daba sama da 30 ne suka kaiwa wani ginin ‘yan sanda hari a lokacin zanga-zangar.
Sanarwar ta tabbatar da cewa jami’in dan sanda guda ne ya rasa ransa sakamakon harin ‘yan dabar da ke dauke da makamai, inda suka kwace bindigogi da harsashai.
Ko da yake gwamnatin Abia ta ce an cafke mutum guda daga cikin maharan, sakamakon raunin da ya samu daga harbin bindiga.
JIHAR EKITI
Shima dai gwamna, Kayode Fayemi ya bayar da umarnin sanya dokar hana fita, bayan da bata gari suka sauyawa zanga-zangar EndSARS suna zuwa rikici.
Gwamnatin dai ta ayyana dokar hana fita ba dare-ba-rana, wadda ta shafi kowanni bangare a ranar Talata.
Gwamnan ya bayyana damuwa kan yadda gangamin #EndSARS da aka soma a cikin lumana ya ya ke neman munana a jihar.
Wanne mataki gwamnatin Najeriya ta dauka?
Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya, Muhammad Adamu, ya bayar da umarnin a baza jami’an ‘yan sandan kwantar da tarzoma a sassan kasar, a wani bangare na shirin ko-ta-kwana.
Sanarwar babban sufeton ‘yan sandan, na zuwa ne bayan samun karuwar tashe-tashen hankula a wasu jihohi sakamakon zanga-zangar neman a rushe rundunar SARS ko kuma SWAT, bayan da aka zargi jami’an sashen da cin zarafin jama’a.
Labarai
Shugabanni ku fito da sabbin dabaru domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta tsadar rayuwa a ƙasa – Human Rights
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights dake jihar Kano, ta ce akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya dace dan ganin an kawo karshen matsalar tsaro, da kuma ta harkar tsaro dake ci gaba da addabar mutane a sassa ƙasar nan.
Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Laraba, ya ce yadda ake ƙara samun ƴan ta’adda suna sace mutane tare da kashe su a sassan ƙasar nan, da kuma halin matsin rayuwar da ake fuskanta akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya kamata dan ganin an kawo ƙarshen matsalolin.
“Yawaitar kai hare-haren da ake samu daga ɓangaren ƴan bindiga a cikin al’ummar gari akan kashe su tare da sace su matuƙar ana son a kawo karshen matsalar, sai an ƙara himma wajen samar da makamai ga jami’an tsaro tare da samar da sabbin dabaru domin kawar da matsalar, “in ji Galadanci”.
Wannan dai na zuwa ne kwanaki kaɗan da sako ɗalibai aƙalla su sama da 285, na makarantar Kuriga dake ƙaramar hukumar Chikun ta jihar Kaduna, da ƴan bindiga suka sace su a baya, baya ga wasu ɗaliban da aka sace a wata makarantar Tsangaya a jihar ta Kaduna, wanda ko a jihar Borno ma aka jiyo yadda aka sace ƴan gudun hijira da dama a baya-bayan nan, inda matsalolin tsaron ke ƙara yin gaba a sassan ƙasar nan.
Labarai
Gwamnan Kano ya kafa kwamitin duba yadda ake rabon tallafin abincin Azumi
Gwamnatin Kano ta kafa kwamitin duba yadda ake ciyarwar azumin watan Ramadan, a kananan hokumomin cikin birnin jihar 8, domin sa ido da duba yadda ake gudanar da aikin dafawa da rabawa al’umma abincin.
Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin ne ƙarƙashin kulawar mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da wasu ƴan kwamitin.
Hakan na zuwa ne dai bayan da gwamna Abba Kabir, ya ziyarci wasu daga cikin wuraren da ake dafa abincin, inda ya nuna rashin jin daɗin sa kan yadda ya ga aikin ke gudana a karamar hukumar kumbotso.
Bayanin hakan ya fito ne ta cikin wata sanarwar da babban mai taimakawa gwamnan Kano, na musamman akan gidajen rediyo Bashir Aminu Fanshekara, ya aikowa manema labarai, ya ce an bayyana Alhaji Danyaro Yakasai, a matsayin wanda zai jagoranci kwamitin mai mambobi 7.
Fanshekara ya ce kwamitin ya fara zagayawa wasu daga cikin mazaɓu dake karamar hukumar kumbotso, domin duba yadda ake dafawa da kuma raba abincin tallafin ga al’umma, inda suka suka fara da mazaɓar Na’ibawa a ranar Asabar 23 ga watan Maris ɗin shekarar 2024.
Ilimi
Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci
Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.
An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.
Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.
Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.
“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.
Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su