Connect with us

Labarai

Zazzabin cizon sauro na yiwa mutanen Afirka dauki dai-dai saboda korona – WHO

Published

on

Hukumar lafiya ta Duniya WHO ta ce tallafin kudade da kuma yadda aka shiga rudani wajen lura da harkokin kiwon lafiya a yankin Kudu da Saharar Afirka, sakamakon cutar Covid-19 ya janyo asarar rayuka da dama, sakamakon zazzabin cizon sauro.

A rahoton da WHO ta fitar ranar Litinin, ta yi gargadi game da illolin da zazzabin cizon sauro ke haifarwa a nahiyar Afirka.

Hukumar ta Majalisar Dinkin DUniya ta ce ta damu matuka kan yadda yaki da annobar corona ke kawo cikas wajen samar da maganin cutar Malaria a nahiyar.

Rahoton da aka fitar ya nuna cewa, an samu raguwar kaso 10 cikin 100 na samar da ingantaccen maganin zazzabin cizon sauro a yankin Afirka, wanda ke iya haifar da karin mutuwar mutane 19,000.

Wannan adadin in ji WHO ya tashi zuwa 46,000 tare da katsewa kusan kashi 25 cikin 100 na samun dama ga akalla mutum 100,000 tallafin maganin zazzabin cizon sauron.

Dakta Matshidiso Moeti, Daraktan WHO a yankin Afirka, ya ce Covid-19 na barazanar dagula kokarin shawo kan matsalar zazzabin cizon sauro, musamman kula da mutanen da ke dauke da cutar.

“Duk da irin mummunar tasirin da Covid-19 ke da shi ga tattalin azrkin Afirka, abokan hulda na kasa-da-kasa, kasashen nahiyar na bukatar kara himma don tabbatar da cewa an fadada shirye-shiryen yaki da zazzabin cizon sauro, wanda ke barazana ga al’ummar yankin.” In ji shi

Rahoton WHO na duniya kan zazzabin cizon sauro, wanda kuma galibi ya shafi kasashen Afirka, ya nuna yadda ake samun koma baya wajen yaki da cutar, sakamakon bullar annobar Covid-19.

 

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending