Connect with us

Labarai

Matuƙar iyaye za su ƙara kula da karatun ƴaƴansu za a samu raguwar ɓata gari – Limami

Published

on

Limamin masallacin Juma’a na Masjid Abubakar Sadeek da ke kan titin unguwar Sheka ɗan tsinke Mallam Usman Muhammad Al’amen, ya yi kira ga iyaye da su ƙara ƙaimi wajen kulawa da karatun ƴaƴansu, domin rayuwarsu ta zamo abar koyi a cikin al’umma.

Mallam Usman Muhammad Yayi kiran ne a yayin saukar karatun Alkur’ani mai girma, makarantar Madarasatul Khairul Anam Littahafiz Qur’an Islamiyya, ta gudanar cikin unguwar Sheka unguwar Kudu dake yankin ƙaramar hukumar Kumbotso, wanda ya gudana ƙarshen makon da ya gabata.

Yana mai cewa, “Matuƙar iyayen zasu ƙara kulawa da karatun ƴaƴansu, babu shakka za’a samu raguwar samun ɓata gari a cikin al’umma, suma kuma matasa musamman ma maza, su ƙara himmatuwa wajen neman ilmin addini dana zamani “Inji Liman Usman Muhammad.

Da yake nasa jawabin Mai unguwar Sheka Unguwar Kudu Mallam Bello Da’u, yabawa ya yi da irin ƙwazon malaman makarantun islamiyyun yankin, inda ya ƙalubalanci matasa maza kan nuna halin ko in kula da suke a kan karatun addinin, “Yakamata su matse damtse wajen neman ilmi “Inji Mai Unguwa Bello.

A nasa jawabin shugaban makarantar, Mallam Shu’aibu Yahya Shu’aibu, kira yayi ga Gwamnati da masu hannu da shuni, da su ƙara himmatuwa wajen tallafawa makarantunsu na Islamiyya, bisa ƙarancin mahalli da kayayyakin karatu da suke fama dasu a cikin makarantunsu.

Wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, Kimanin ɗalibai 21 ne sukayi saukar, daga ciki kuwa akwai mata 17 maza 4.

Labarai

Ƙudurin gyaran dokar gudanarwar Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi ya tsallake karatu na ɗaya a majalisar dokokin Kano

Published

on

Ƙudurin gyaran dokar gudanarwar Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke jihar Kano, ya tsallake karatu na ɗaya a zauren majalisar dokokin jihar.

Ƙudurin ya kai wannan mataki ne yayin zaman majalisar na yau Laraba, ƙarƙashin jagorancin shugaban majalisar Alhaji Jibril Isma’il Falgore, bayan da akawun majalisar Alhaji Bashir Idris Ɗiso, ya gabatar da karatun na ɗaya.

Har ila yau, yayin zaman na yau, majalisar ta buƙaci gwamnatin Injiniya Abba Kabir Yusuf, da ta tallafa wa wasu kanikawa da kafintoci bisa iftila’in gobarar da ta ƙone musu kaya na miliyoyin Naira, tare da asarar rayuka a kan titin Lawan Dambazau.

Majalisar ta buƙaci hakan ne biyo bayan ƙudurin gaggawa da wakilin ƙaramar hukumar Birni da kewaye Alhaji Sarki Aliyu Daneji ya gabatar.

Yayin gabatar da ƙuɗurin, ɗan majalisar ya nemi gwamnatin data tallafa wa waɗanda gobarar ta shafa domin rage musu raɗaɗin iftila’in.

Majalisar ta kuma bukaci gwamnatin da ta ɗaga darajar asibitin garin Gano, zuwa matakin babban asibiti domin ƙara inganta kiwon lafiya a yankin har ma da sauran yankuna, kamar yadda ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Shu’aibu Rabi’u ya buƙata.

Wakilinmu na majalisar Auwal Hassan Fagge, ya ruwaito cewa, a dai zaman na yau Laraba, shi ma ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ƙaraye, Injiniya Ahmed Ibrahim, ya gabatar da ƙudurin neman gwamnatin Kano ta gina titi a hanyar da ta tashi daga mahaɗar titin zuwa sansanin horas da matasa ƴan hidimar ƙasa, ta bi ta Kurugu da Dederi har zuwa Yammedi duk a yankin ƙaramar hukumar Ƙaraye.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya sauya shugaban hukumar tattara haraji na jihar

Published

on

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin Dakta Zaid Abubakar, a matsayin sabon shugaban hukumar tattara kuɗaɗen haraji ta jihar Kano, da kuma Kasim Ibrahim a matsayin babban daraktan hukumar.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar da aka aikowa Dala FM Kano, a daren jiya Laraba.

Sanarwar ta ce, tsohon shugaban hukumar Alhaji Sani Abdulkadir Dambo, an mayar da shi ne a matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin zuba jari, wanda kuma sauye-sauyen za su fara aiki nan take.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur: Fadar shugaban ƙasa kiyi wani abu dan mutane su samu sauƙi – Ƙungiyar Nothern Concern Soliderity

Published

on

Yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar wahalar man fetur a ƙasar nan, ƙungiyar da ta damu da abubuwan da suka shafi arewacin ƙasar nan ta Northern Concern Soliderity, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi abinda ya dace dan ganin mutane sun samu wani sauƙi.

Babban jami’in gudanarwar ƙungiyar, kuma sakataren riƙo na zauren gamayyar kungiyoyin Arewacin Najeriya, Kwamared Saddat Usman Maiyaƙi, ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, lokacin da yake nuna takaici kan irin wahalar da al’ummar ƙasa suke sha wajen shan man Fetur a gidajen man.

Ya ce duba da halin matsin rayuwar da al’umma suka samu kansu a ciki, akwai buƙatar shugabanni da masu ruwa da tsaki su kawo ƙarshen wahalar man Fetur ɗin da aka fama da ita.

Kwamared Saddat Maiyaƙi, ya kuma haƙurƙurtar da al’ummar ƙasar nan kan halin ƙuncin rayuwar da suka samu kai a ciki, inda ya yi fatan komai ya zo karshe cikin ƙanƙanen lokaci.

Continue Reading

Trending