Connect with us

Labarai

Shekarar 2020: Gidaje 46,000 suka lalace a Kano sakamakon ambaliyar ruwan sama – SEMA

Published

on

Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Kano SEMA ta ce ambaliyar ruwa a shekarar 2020 ta yi sanadiyyar lalacewar gonaki sama da 10, 000 sakamakon mamakon ruwan sama da aka yi.

Yayin da ambaliyar ta yi sanadiyyar rayukan mutane 56 sai kuma mutane 100 da gini ya faɗo a kansu, da dama kuma suka jikkata.

Shugaban hukumar Kwamared Sale Aliyu Jili ne ya bayyana hakan yayin zantwarsa da Freedom Rediyo.

Jili ya ce, a bana kimanin gidaje 46,000 ne suka lalace sakamakon mamakon ruwan sama da aka samu.

Yana mai cewa an samu ambaliyar ruwa a ƙananan hukumomi 44 na jihar Kano, ba kamar yadda hukumar hasashen masana yanayi ta ce ƙananan hukumomi 23 ba kawai.

Idan dai za a iya tunawa tun kafin saukar damunar a bana, hukumar hasashen masana yanayi ta ƙasa NIMET ta ce “kimanin ƙananan hukumomin jihar Kano 23 za su samu ambaliyar ruwa a shekarar”.

Jili, ya ƙara da cewa, wannan adadi da aka samu na ƙaruwar ambaliyar ruwa ya janyo gwamnati ta gaza wajen magancewa waɗanda ibtila’in ya shafa halin da suke ciki.

Labarai

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa Saudiyya

Published

on

Yanzu haka hukumar Aikin Hajji ta ƙasa NAHCON, ta 15 ga watan nan na Mayun 2024, a matsayin ranar da za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana, zuwa ƙasa mai tsarki.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin shugaban hukumar ta NAHCON, Jalal Ahmad Arabi, a wajen taron masu ruwa da tsaki kan aikin Hajji da Umrah, da ya gudana yau Alhamis birnin tarayya Abuja.

“Maniyyata kimanin 65,500 ne za su sauke Farali daga ƙasar nan a ƙasa mai tsarki; za su shafe aƙalla kwanaki huɗu domin yin ziyara a Madina kafin fara aikin Hajji, “in ji Arabi”.

Daga bisani shugaban hukumar aikin hajjin Jalal Ahmad Arabi, ya kuma bayyana cewa za ayi jigilar maniyyata aikin hajjin ne daga cibiyoyi 10 a faɗi ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Trending