Connect with us

Labarai

Tsaiko: Abduljabbar ya zargi gwamnatin Kano a kan shari’a

Published

on

A yau Laraba 28-07-2021, babbar kotun shari’ar muslinci ta birni a jihar Kano ta ci gaba da sauraron Shari’ar nan wadda gwamnatin Kano ta gurfanar da Malam Abduljabbar Nasiru Kabara.

Gwamnatin ta na zargin malamin da laifin batanci ga fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (S.A.W).

A zaman kotun na yau mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola, ya tambayi lauyan gwamnati cewar a zaman da kotun ta yi a baya wanda a ke tuhuma ya musanta zargin da ake masa, domin haka ko kun zo da shaidun.

A nan ne lauyar gwamnati ta shaidawa kotun cewar ba su zo da shaidun ba, domin suna bukatar su rubuta tuhuma daga ma’aikatar Shari’a tun da yanzu takarda tuhuma ta ‘yansanda ce kawai a gaban kotun.

A nan ne lauyan da ya ke kare Abduljabbar, Barrister Sale Muhammad Bakoro, ya bayyana wa kotun cewar masu kara suna son kawo tsaiko tunda Wanda ake Kara ya na tsare a gidan gyaran hali yau kwanaki 12 kenan, amma a ce har yanzu ba su shirya takarda tuhuma ba.

Saboda haka barrister Sale Bakoro ya roki kotun a kan cewar in har kotun za ta daga zaman, to kotun ta umarci masu kara su basu duk wasu takardu da su ka shafi Shari’ar da sunan shaidun da kuma duk wani abu wanda zai taimakawa wanda ake tuhuma, domin kare kansa.

A nan ne lauyar gwamnati ta bayyanawa kotun cewar lauyan wanda ake kara ya yi azarbabi dama duk wannan roke-roke da ya yi munsan su kuma da zarar mun gabatar da tuhuma zai ga mun kawo duk abubuwan da ya roka, domin haka ta jaddada rokonta akan a sanya wata rana.

Labarai

Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama

Published

on

Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.

Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.

Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.

Continue Reading

Labarai

Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam

Published

on

Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.

Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.

Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.

Continue Reading

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Trending