Connect with us

Labarai

Zargin kisan kai: Kotu ta aike da matashi gidan gyaran hali

Published

on

Kotun Majistret mai lamba 70 karkashin mai Shari’a, Faruk Umar Ibrahim, ta aike da wani matashi gidan gyaran hali har zuwa ranar 24 ga wannan watan na shekarar 2021.
Matashin mai suna, Nura Usman Dandago, wanda a ka fi sani da Ribado, a na zargin shi da laifin kisan kai da samun sa da makami laifukan da suvka saba da sashi na 221 da na 319 na kundin penal code.
Kunshin zargin ya bayyana cewar, a ranar 22 ga watan da ya gabata wani mutum mai suna, Malam Yakubu Abdullahi, ya yi korafi a wajen ‘yansanda a kan cewar, wanda a ke zargin, Nura Usman, ya kashe mai Dansa mai suna, Mujittafa Yakubu Abdullahi.
Kunshin zargin ya bayyana cewar, an yi kisan ne da wata wuka Mai kaifi, a, yayin da a ka karanta kunshin zargin, kotun ta bayyanawa wanda a ke zargi cewar ba ta da hurumin yi masa shari’a, domin haka ya na da damar daukar lauya kamar yadda doka ta tanada, amma wannan kotu ba da hurumi sai dai a jira zuwa lokacin da ma’aikatar shari’a za su rubuta takardar tuhuma zuwa babbar kotun jiha.
Wakilin mu, Yusuf Nadabo Ismail, ya rawaito mana cewar, mai Shari’a, Faruk Ibrahim, ya yi umarni a tsare wanda a ke tuhumar, har zuwa ranar 24 ga wannan watan.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending