Connect with us

Labarai

Hukumar Yaki da Cutar Kanjamau a Kano ta wayar da kan dalibai a kan illar cutar

Published

on

Hukumar Yaki da Cutar Kanjamau ta Jihar Kano ta wayar da kan daliban kwalejin ilimi ta Sa’adatu Rimi, kan illar cutar kanjamau, ciwon hanta da daliban manyan makarantun gaba da sakandare da kuma muhimmancin tantancewa kafin aure da aka gudanar a dakin taro na kwalejin.

Hukumar ta shirya laccar ne, domin kara wayar da kan matasa kan cutar kanjamau da kuma rigakafin cutar ciwon hanta a tsakanin matasa da suka fi fama da rauni.

Darakta Janar na hukumar, Dr. Sabitu Y. Shu’aibu Shanono, ya ce, hukumar ta himmatu wajen cimma burin Majalisar Dinkin Duniya ta hanyar kawo karshen kamuwa da sabbin kwayoyin cuta guda biyu a shekarar 2030.

Ya ce,”Hukumar ta ba da fifiko kan al’amuran da suka shafi hana kyama da nuna wariya da karfafa yin gwajin kafin aure da kuma mace mai juna biyu domin rigakafin kamuwa da cutar kanjamau daga uwa zuwa yara”. In ji Dr. Sabitu

Darakta Janar wanda Daraktar Kula da Rigakafi da Kula da Lafiya ta Jihar, Dr. Sa’adatu Sale ta wakilta a wajen taron ta bukaci daliban da su mika muhimman bayanan da suka samu ga takwarorinsu, ‘yan uwa da sauran al’umma.

 

Labarai

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa Saudiyya

Published

on

Yanzu haka hukumar Aikin Hajji ta ƙasa NAHCON, ta 15 ga watan nan na Mayun 2024, a matsayin ranar da za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana, zuwa ƙasa mai tsarki.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin shugaban hukumar ta NAHCON, Jalal Ahmad Arabi, a wajen taron masu ruwa da tsaki kan aikin Hajji da Umrah, da ya gudana yau Alhamis birnin tarayya Abuja.

“Maniyyata kimanin 65,500 ne za su sauke Farali daga ƙasar nan a ƙasa mai tsarki; za su shafe aƙalla kwanaki huɗu domin yin ziyara a Madina kafin fara aikin Hajji, “in ji Arabi”.

Daga bisani shugaban hukumar aikin hajjin Jalal Ahmad Arabi, ya kuma bayyana cewa za ayi jigilar maniyyata aikin hajjin ne daga cibiyoyi 10 a faɗi ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Trending