Connect with us

Manyan Labarai

Na dan ji ba dadi da ka ja da ni a takarar fidda gwani – Tinubu

Published

on

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Bola Ahmad Tinubu, ya ce, ya ji dan ba dadi da Sanata Ahmad Lawan shugaban majalisar dattawa ya ja da shi a zaben fidda gwani.

Tinubu ya bayyana hakan ne yayin jawabinsa, bayan ya samu nasara a zaben fidda gwani na jam’iyyar APC a Abuja.

Tinu bu ya kuma ce”Abun kunya ne ga wadanda suke so su ga faduwar jam’iyyar APC a zaben 2023, domin kuwa APC na nan yadda take daram”.

“Shiru-shirun da na yi ba tsoro bane gudun magana ne, kuma a yanzu mun shirya gwabzawa da ko waye”.

“Shekaru 16 da PDP ta yi ta na barna a fadin kasar nan, yanzu ne lokaci ya yi da zamu samar da sabuwar Najeriya ga ‘ya’yan mu”

“Mu masu son ci gaba ne, mu masu son gina kasa ne, mu masu son kawar da duk wani abu da ya shafi kasar nan da al’ummar mu, mun shirya kawar da duk wanda ya shige mana gaba, gwamnonin da suka zabe ni ban san mai na yi na kirki da suka zabe ni ba, amma na san domin ci gaban kasa suka zaben ni. Za mu ci gaba da yakar duk wanda ya kawo tsaiko a Najeriya”.

“Yau rana ce da mata na 2, musamman ma Mama 60, bisa kwana da ta yi cir idanun ta biyu, ina godiya a gare ku”.

“Shugaban kasa ka yi hakuri da na sa ka kwana idanu biyu cir a wajen nan, kuma wannan lokaci ne ni ma da ya kamata ka rama min, tun da a baya ni ma na yi maka haka”.

 

Labarai

Mu yawaita karanta Alƙur’ani da aikin alkhairi a watan Ramadan – Malam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallaacin Juma’a na Salafussalih dake unguwar Ɗorayi ƙarama Malam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’ummar musulmi da su ƙara himma wajen karanta Al-ƙur’ani mai girma, tare da aikata ayyukan alkhairi domin rabauta da rahamar Allah S.W.T a nan duniya dama gobe ƙiyama.

Mallam Ibrahim Bunkure ya bayyana hakan ne lokacin da yake tsokaci kan huɗubar Juma’ar da ya gabatar yau a masallacin.

Ya ce, kamata yayi musulmai su ƙara yin koyi da kyawawan ɗabi’un Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama, domin zama ababen koyi a rayuwa.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya kuma shawarci al’umma da su ƙara kasancewa masu yafiya musamman a lokacin da aka yi mutu abinda bai musu daɗi ba, bisa mahimmancin da hakan yake da shi.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gawuna ya taya Abba Gida Gida murna

Published

on

Dan takarar Gwamnan Kano na jam’iyyar APC a zaben 2023 Dakta Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana karbar kaddara tun bayan da ya Fadi zaben 18 ga watan Maris.

Cikin Wani Sakon murya, Dakta Nasiru Gawuna ya godewa magoya baya, tare da yin fatan alkhairi ga sabuwar gwamnati.

” Wannan sabuwar gwamnati Allah ya Bata ikon yiwa al’umma adalchi, mu Kuma Allah ya bamu ikon yin biyayya.”

 

 

Continue Reading

Manyan Labarai

Abba Gida Gida ya karbi shaidar lashe zabe

Published

on

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabiru Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida gida ya karbi shaidar lashe zaben Gwamnan Kano.

Ya karbi wannan shaida ce yayin wani taro da hukumar INEC ta shirya domin bashi shaidar satifiket, bayan nasarar da ya samu a zaben ranar 18 ga watan Maris 2023.

Taron dai Wanda ya samu halartar da dama daga cikin manyan jihar Kano dama shiyyar arewa maso yamma, ya gudana ne a dakin taro na ofishin hukumar zabe INEC na jihar Kano.

Continue Reading

Trending