Labarai
Karanta Labaran Dala na Yau Alhamis 18-04-2019

Karanta Labaran Dala na Yau Alhamis 18-04-2019
LABARAI A TAKAICE
Wani masanin zamantakewar dan adam dake Kwalejin Sa’adatu Rimi, Kwamared Auwal Rabi’u Babban Wando ya ce dabi’ar daukar hoto kafin aure wato pre-wedding pictures wanda matasa ke yi, bakuwar al’ada ce da suke kwaikwayo daga turawa wadda kuma zata iya bata rayuwar al’umma a wanan lokaci matukar ba’a kaurace yin hakan ba.
Kwamared Auwal Rabi’u Babban Wando ya bayyana hakan ne a ganawarsa da gidan Radiyon Dala, yana mai cewa shekarun girma da matasan suke kai, shi ne ke jan hankalin su wajen karkata kan al’amuran da suka shafi biyan bukatar sha’awa dake tsakanin mabambanta jinsi.
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, ta bukaci al’umma da su rinka sanar dasu rahoton faruwar hadari domin kai daukin gaggawa cikin al’amarin kasancewar ya na daya daga cikin aikin hukumar.
Jami’in hulda da jama na hukumar, PFO Sa’idu Muhammad Ibrahim ne ya yi wannan kiran yayin ganawarsa da wakilin mu Hassan Mahmuda Ya’u, a kan wani kira da suka samu cikin dare sakamakon wani hadari da ya auku a kan titin Sharada, wanda ya jikkata wani mai babur yayin da suka yi taho mu gama da mai mota karshe a ka mika su zuwa asibiti cikin wani hali don ceto rayuwarsu.
Hukumar Hisba a nan jihar Kano, ta gargadi masu bada hayar gidaje dasu daina bada hayar gidaje ga mata masu zaman kansu ko kuma gauraya su da matan aure wuri guda.
Mataimakin hukumar kan nazarin manyan laifuka, Malam Idris Ibn Umar ne yayi wannan gargadi biyo bayan wani korafi da wata matar aure ta yi kan cewa wani mai bada hayar gidaje ya hadasu gida guda da mata masu zaman kansu inda ta bukaci ya sauya mata gida ko ya ba ta kudin ta abin ya gagara.
LABARAN DALA
18 04 2019.
LABARAI A TAKAICE.
Kakakin hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa a nan kano, Kabiru Ibrahim Daura, ya gargadi fasinjoji dasu kauracewa hawa motar da aka yiwa kazamin lodi da kuma masu gudun wuce sa’a, domin kiyaye rayuwarsu da kuma lafiyarsu.
Kabiru Ibrahim daura ya yi wanan jan hankalinne a ganawarsa da gidan radiyon Dala, kan wani hadari da kazamin lodi da gudun wuce sa’a suka haddasa, a ranar shida ga wannan watan kan titin zuwa Dan-batta, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane uku, bakwai kuma suka jikkata.
Rundunar ‘yan sandan jihar kano tace ta shirya tsaf don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’aumma ya yin gudanar da bukukuwan good Friday da Ista Monday.
Wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai Magana da yawun rundunar DSP Abdullai Haruna, ta rawaito cewa, rundunar ta kuma bukaci mutane su sanya ido kan bakin al’amrura tare kai rahoton duk wani abu da basu yarda dashi ba ga ofishin yansanda mafi kusa, tana mai jaddada haramcin fasa knock out yayin bukukuwan.
Mai Magana da yawun kotunan jihar kano baba jibo Ibrahim ya ce babban jojin jihar kano justice Nura Sagir Umar, ya bada hutu ga manayan alkalan kotunan jihar kano daga yau 18 ga watan Afirilu zuwa ranar 29 ga watan.
A zantawarsa da gidan radiyon Dala, Baba jibo Ibarahim ya ce hutun wanda bai shafi kotunan shari’ar musulinci ba, tanadi ne na kundin dokar tafikar da kotunan jihar kano ta shekarar 2014, karkashin oda ta 45.
Kotun Majistret dake zaman ta a Noman Sland a nan Kano, ta gurfanar da wasu mutane bakwai ciki harda wani mutum mai suna Muhammad Muntari, wanda ake zargin su da aikata laifuka wanda suka hada da mallakar manyan makamai ba bisa ka’ida ba da kuma yin fashi da makami tare da yunkurin yin garkuwa da mutane don neman kudin fansa.

Labarai
Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.
Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.
Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.
Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.
A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Labarai
Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.
Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.
“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.
Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.
Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Labarai
Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.
Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.
Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.
Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su