Labarai
LABARAN DALA22 04 2019

LABARAN DALA
22 04 2019
LABARAI A TAKAICE
Dan dakan Karaye, kuma babban sakataren hukumar inganta tarihi da al’adun jihar Kano, Ibrahim Mua’azu, ya bukaci iyaye da su kasance masu kula da tarbiyyar ‘ya’yan su domin inganta rayuwar su.
Ibrahim Mu’azu, ya yi wannan kiran ne yayin bikin saukar karatun al’kurani mai girma na makarantar Abu Hurairai Islamiyya dake Lokon Makera a unguwar Kofar Na’isa.
Babban limamin Masallacin Juma’a na Sheikh Jafar Mahmud Adam, dake unguwar Sabuwar Gandu, Mallam Abdullah Ishaq Abdullahi Garangamawa, ya yi kira ga al’umma dasu tashi tsaye wurin neman illimin addinin musulinci domin samun ingantaciyyar rayuwa da kuma tsira a gobe kiyama.
Malam Abdullah Ishaq Abdullah, ya yi wannan kiran ne yayin saukar Alkur’ani mai girma da makarantar Sheikh Jafar Mahmud Adam ta gudanar a unguwar Sabuwar Gandu a karshen makon da ya gabata.
A nan kuma limamin masallacin juma’a na Annur dake unguwar Zawachiki a karamar hukumar Kumbotso, Mallam Babangida Abba Giyade, bayyana cewa zance da ‘yan mata da samari ke yio kafin neman aure ba shine abin da musulunci ya bada umarni a yi ba, kawai dai jama’a na yi ne bisa masalahar kansu.
Mallam Babangida Abba Giyade, ya bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala shirin matattar Alheri na gidan rediyon Dala, ya ce ya kamata yayi a fara neman abokiyar zama kafin a yi aure.
Shugabar kungiyar tallafawa ‘yan gudun hijira ta Binta Muhammad Lawan ta yi kira ga sauran kungiyoyin al’umma da su rinka tallafawa ‘yan gudun hijira dake fadin jihar Kano baki daya.
Shugabar kungiyar Binta Muhammad ta bayyana hakan ne yayin rabon tallafin kayan more rayuwa da kungiyar ta rabawa ‘yan gudun hijira su kimanin 100 da suka ci gajiyar tallafin a sansanin su na dake unguwar Hotoro a nan Kano.
A wani labarin kuma wata kungiya mai rajin yaki da barace-barace, ta ja hankalin iyaye cewa dasu sauke nauyin da A… ya daura masu wurin lura da tarbiyyar ‘ya’yan su maimakon tura su yawon bara.
Babban jami’in gudanarwa na kungiyar reshen jihar Kano, Kwamrade Aliyu Samba ne yayi wannan kiran yayin taron gangamin wayar da kan iyaye kan barace-barace da kungiyar ta gudanar irin sa na farko a nan Kano.
Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kama wasu mutane hudu dauke da bindiga da wasu mutane biyu su na hadiyar hodar iblis a wani Otel a nan Kano a yunkurin su na safararta zuwa kasar Sudan da kuma kasar Saudiyya.
Da yake holin mutanen a karshen makon da ya gabata kwamandan hukumar ta NDLEA a nan Kano, Dr Ibrahim Abdul, ya bayyanawa manema labarai cewa kimanin watanni biyu suka shafe suna bibiyar masu yunkurin safarar hodar iblis din, wakilin mu Abba Isah Muhammad ya rawaito cewa hukumar na kara neman hadin kai daga ‘yan kasa na gari.
Takaitattun labaran Dala Kenan….
Kada ku manta zaku iya samun sabbin labaran da muke sabintawa tsawon awanni ashirin da hudu a shafinmu na internet wato www.dalafmkano.com
Haka kuma zaku iya bayyana ra’ayoyinku ko tafka muhawara akan batutuwan da muke tattaunawa a dandalin Facebook da Twitter a Dala FM Kano.

Labarai
Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.
Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.
Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.
Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.
A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Labarai
Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.
Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.
“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.
Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.
Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Labarai
Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.
Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.
Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.
Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su