Connect with us

Manyan Labarai

Takarar Muslumi da Musulmi: Lauya ya kai karar APC da Tinubu kotu

Published

on

Wani lauya mazaunin Abuja, Osigwe Momoh, ya maka jam’iyyar APC da dan takararta na shugaban kasa, Bola Tinubu kara, a kan tsayar da musulmi dan takarar mataimakin shugaban kasa.

Tinubu ya zabi Kashim Shettima, tsohon gwamnan Borno, a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023. Wannan ci gaban ya haifar da fushi daga manyan masu ruwa da tsaki, musamman kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN).

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1188/2022 da aka shigar a gaban wata babbar kotun tarayya dake Abuja, Momoh na neman a ba da umarnin har abada hukumar zabe ta kasa (INEC) daga buga sunan Tinubu a zabe mai zuwa.

Ya ce, jam’iyyar APC ta saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya, ta hanyar zabo dan takararta na shugaban kasa da abokin takararsa daga addini daya.

A farkon sammacin, mai shigar da karar ya bayyana cewa, bisa ga babi na biyu na kundin tsarin mulkin tarayya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima), dole ne jam’iyyun siyasa su samu ‘yan takararsu na shugaban kasa da na mataimakin shugaban kasa daga bangarori daban-daban na kabilu da na addini.

Saboda haka, ya roki kotun da ta bayyana cewa, “Bisa ga sashi na 14 (1) & (3), 15 da 224 (a) na kundin tsarin mulkin tarayya na 1999, (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima), wadanda ake kara suna da hakkin su. Ka’idojin Babi na II na Kundin Tsarin Mulki na 1999 kamar yadda aka gyara da samun ‘yan takarar shugaban kasa da mataimakan shugaban kasa na addini daya ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa kuma ba komai bane”.

Momoh yana kuma neman odar “Soke takarar APC, Tinubu (daya cikin 2), wanda ya sabawa kundin tsarin mulki kuma ya saba wa ruhin sashe na 14 (1) & (3), 15 da 224 (a) na 1999 da aka gyara. Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya”.

Har yanzu ba a sanya ranar da za a saurari karar ba.

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Manyan Labarai

An ga watan ƙaramar Sallah a Najeriya – Sarkin Musulmi

Published

on

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na uku ya tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya, inda za a yi karamar Sallah gobe Lahadi.

Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yayin jawabin da ya gabatar a cikin daren Asabar ɗin nan, ya ce sun samu rahotannin ganin watan ne daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

Alhaji Sa’ad Abubakar ya ce daga cikin guraren da aiko musu da ganin jinjirin watan na Shawwal akwai Zazzau, da kuma daga Sarkin Dutse, da Arugungu, da kuma Shehun Borno, da dai sauran gurare daban-daban na Najeriya.

Ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su gabatar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali, tare da taimaka wa mabuƙata.

Tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewa, biyo bayan sanarwar fadar mai alfarma Sarkin Musulmi, ya kasance ranar Lahadi take 1 ga watan Shawwal na shekarar 1446, wato ranar ƙaramar Sallah.

Continue Reading

Manyan Labarai

Shugaba Tinubu da Sifeton Ƴan Sanda ku bi wa mutanen mu da aka yi wa kisan gilla hakƙin su – Rt. Hon. Rurum

Published

on

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Rabo, Kibiya da Bunkure, Kabiru Alhassan Rurum, ya bayyana kaɗuwar sa bisa kisan gillan da aka yi wa wasu Mafarauta su kusan 16, a garin Uromi da ke jihar Edo, a lokacin da suke hanyar su ta komawa Kano daga jihar Rivers.

Honarable Kabiru Rurum, ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da aka aikowa Dala FM Kano a ranar Asabar, ya ce daga cikin mutanen da aka ƙona akwai mutum 11 da suka fito daga mazaɓun yankin sa na Kibiya da Bunkure, inda wasu 6 suka samu muggan raunuka suna karɓar Magani yanzu haka a jihar Edo.

A cewar Ɗan Majalisar, “Wannan abu da matasan garin Uromi a jihar Edo, suka yi ya saɓa da dokar kasa, kuma mummunan laifi ne, a don haka za mu bi kadin hakƙin mutanen mu da aka kashe a kuma waɗanda aka jikkata, “in ji shi“.

Kabiru Rurum, ya ce a matsayinsa na wakilin mutanen da aka kashe a majalisar Wakilai ta ƙasa, yana kira ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, da babban Sifeton ƴan sanda, da su yi duk mai yiyuwa wajen ganin an kamo waɗanda suka yi wannan aika-aikar tare da hukunta su, da kuma biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu da kula da waɗanda suka jikkata.

“Kasancewar wannan bashi ne na farko da ake samun wasu ɓata gari na tare matafiya akan hanya da basu ji ba basu gani ba su kashe su, a don haka muna fatan wannan karon gwamnati da sauran hukumomin tsaro za su ƙaddamar da ƙwaƙƙwaran bincike don ɗaukae mataki kamar yadda dokar kasa ta tanada, “in ji Rurum”.

Ɗan majalisar ya kuma jajantawa dukkanin al’ummar jihar Kano musamman Iyalan waɗanda suka rasu, tare da addu’ar Allah ya gafarta musu yasa Jannatul Firdausi makomar su, su kuma waɗanda suka jikkata Allah ya basu lafiya.

Continue Reading

Trending