Connect with us

Manyan Labarai

Takarar Muslumi da Musulmi: Lauya ya kai karar APC da Tinubu kotu

Published

on

Wani lauya mazaunin Abuja, Osigwe Momoh, ya maka jam’iyyar APC da dan takararta na shugaban kasa, Bola Tinubu kara, a kan tsayar da musulmi dan takarar mataimakin shugaban kasa.

Tinubu ya zabi Kashim Shettima, tsohon gwamnan Borno, a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023. Wannan ci gaban ya haifar da fushi daga manyan masu ruwa da tsaki, musamman kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN).

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1188/2022 da aka shigar a gaban wata babbar kotun tarayya dake Abuja, Momoh na neman a ba da umarnin har abada hukumar zabe ta kasa (INEC) daga buga sunan Tinubu a zabe mai zuwa.

Ya ce, jam’iyyar APC ta saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya, ta hanyar zabo dan takararta na shugaban kasa da abokin takararsa daga addini daya.

A farkon sammacin, mai shigar da karar ya bayyana cewa, bisa ga babi na biyu na kundin tsarin mulkin tarayya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima), dole ne jam’iyyun siyasa su samu ‘yan takararsu na shugaban kasa da na mataimakin shugaban kasa daga bangarori daban-daban na kabilu da na addini.

Saboda haka, ya roki kotun da ta bayyana cewa, “Bisa ga sashi na 14 (1) & (3), 15 da 224 (a) na kundin tsarin mulkin tarayya na 1999, (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima), wadanda ake kara suna da hakkin su. Ka’idojin Babi na II na Kundin Tsarin Mulki na 1999 kamar yadda aka gyara da samun ‘yan takarar shugaban kasa da mataimakan shugaban kasa na addini daya ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa kuma ba komai bane”.

Momoh yana kuma neman odar “Soke takarar APC, Tinubu (daya cikin 2), wanda ya sabawa kundin tsarin mulki kuma ya saba wa ruhin sashe na 14 (1) & (3), 15 da 224 (a) na 1999 da aka gyara. Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya”.

Har yanzu ba a sanya ranar da za a saurari karar ba.

Manyan Labarai

Bamu da wata alaƙa akan dakatar da Ganduje daga jam’iyyar APC – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya ce basu da wata alaƙa da rikicin cikin gidan da ya kunno kai akan dakatar da Ganduje daga cikin jam’iyyar APC, a Kano.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM a yau Laraba.

Ya ce zargin da jam’iyyar APCn Kano ta yi a kan gwamnatin Kano, kan cewar tana da hannu akan dakatar da shugaban ta na riƙo a matakin ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, zargin bashi da tushe ballantana makama.

A baya-bayan nan ne dai wani sashi na shugabancin jam’iyyar APC, a mazaɓar Ganduje da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, ya bayyana dakatar da Abdullahi Ganduje daga cikin jam’iyyar.

Sai dai daga bisani shugaban jam’iyyar na ƙaramar hukumar ya musanta batun dakatarwar inda ya ce ana shirin ɗaukar matakin da ya dace akan wanda ya fitar da sanarwar.

Bature, ya kuma ce lamarin rikici ne na cikin gidan jam’iyyar ta APC, wanda ya kamata su tsaya su gyara, mai-makon mayar da hankali akan gwamnatin Kano, lamarin da ba za suyi nasara ba.

“Tsagin jam’iyyar APCn, Kano suje can kada su ƙara tsomo mu a cikin rikicin su domin bamu da alaƙa da wani rikicin su ko wani abu, “in ji Sunusi”.

Ya kuma ce ko da yaushe jam’iyyar NNPP, mai mulki a jihar Kano burin su shine ci gaba da taimakawa al’ummar jihar ta hanyar damar da ayyukan ci gaban su.

Dawakin Tofa, ya kuma ƙara da cewa Ganduje bashi da tasiri ko da a ƙaramar hukumar sa ballantana kuma azo batun jahar Kano.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Manyan Labarai

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf

Published

on

Tsagin jam’iyyar NNPP ta ƙasa karkashin jagorancin Major Agbo, ya sanar da dakatar da Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf daga cikin jam’iyyar.

A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar ta ƙasa Ogini Olaposi, ya fitar a yayin taron ‘yan jarida a Talatar nan a Abuja, tsagin jam’iyyar ta NNPP, ya ce rashin bayyana a gaban kwamitin ladabtarwar jam’iyyar da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yi shine ya sanya su ɗaukar wannan mataki.

Ya ƙara da cewa matakin na zuwa ne sakamakon fusata da jam’iyyar ta yi kan halartar wani babban taron jam’iyyar da gwamnan ya yi wanda tsagin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya jagoranta a ranar 6 ga watan Afrilun nan na shekarar 2024. kamar yadda jaridar THE PUNCH ta rawaito.

Sai dai tuni wasu ƴan Kwankwasiyyar suka yi watsi da wannan dakatarwa.

Dambarwar dai na zuwa ne yayin da itama jam’iyyar APC, ke ci gaba da fuskantar ta ta dambarwar, musamman ma da aka jiyo yadda wani sashi na shugabancin jam’iyyar a mazaɓar Ganduje a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, aka jiyo shi ya dakatar da shugaban riƙo na APC ta ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, daga cikin jam’iyyar.

Sai dai daga bisani shugabancin jam’iyyar ta APC, a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa, ya musanta batun dakatarwar lamarin da yace ma ana shirye-shiryen ɗaukar mataki akan waɗanda suka bayyana dakatarwar.

Continue Reading

Trending