Connect with us

Manyan Labarai

Takarar Muslumi da Musulmi: Lauya ya kai karar APC da Tinubu kotu

Published

on

Wani lauya mazaunin Abuja, Osigwe Momoh, ya maka jam’iyyar APC da dan takararta na shugaban kasa, Bola Tinubu kara, a kan tsayar da musulmi dan takarar mataimakin shugaban kasa.

Tinubu ya zabi Kashim Shettima, tsohon gwamnan Borno, a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023. Wannan ci gaban ya haifar da fushi daga manyan masu ruwa da tsaki, musamman kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN).

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1188/2022 da aka shigar a gaban wata babbar kotun tarayya dake Abuja, Momoh na neman a ba da umarnin har abada hukumar zabe ta kasa (INEC) daga buga sunan Tinubu a zabe mai zuwa.

Ya ce, jam’iyyar APC ta saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya, ta hanyar zabo dan takararta na shugaban kasa da abokin takararsa daga addini daya.

A farkon sammacin, mai shigar da karar ya bayyana cewa, bisa ga babi na biyu na kundin tsarin mulkin tarayya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima), dole ne jam’iyyun siyasa su samu ‘yan takararsu na shugaban kasa da na mataimakin shugaban kasa daga bangarori daban-daban na kabilu da na addini.

Saboda haka, ya roki kotun da ta bayyana cewa, “Bisa ga sashi na 14 (1) & (3), 15 da 224 (a) na kundin tsarin mulkin tarayya na 1999, (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima), wadanda ake kara suna da hakkin su. Ka’idojin Babi na II na Kundin Tsarin Mulki na 1999 kamar yadda aka gyara da samun ‘yan takarar shugaban kasa da mataimakan shugaban kasa na addini daya ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa kuma ba komai bane”.

Momoh yana kuma neman odar “Soke takarar APC, Tinubu (daya cikin 2), wanda ya sabawa kundin tsarin mulki kuma ya saba wa ruhin sashe na 14 (1) & (3), 15 da 224 (a) na 1999 da aka gyara. Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya”.

Har yanzu ba a sanya ranar da za a saurari karar ba.

Manyan Labarai

Babu ɗaga Ƙafa tsakanin mu da Ƴan Daba da masu ƙwacen Waya a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Wayoyin jama’a da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye ta Anty Snaching Phone, ta gargaɗi matasan da suke addabar al’umma da faɗan Daba a cikin birnin jihar Kano, da su ƙauracewa hakan domin ba za su saurarawa dukkanin wanda ya faɗa komar su ba.

Kwamandan rundunar tsaron a jihar Kano Inuwa Salisu Sharaɗa, shi ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, ya ce duk wanda suka kama da laifi musamman ma na faɗan Daba, ko ƙwacen waya ko kuma sha da dillancin kayan maye, za a ɗauki tsattsauran mataki akan sa.

 

“Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu ƙwacen Wayoyin jama’a, da Faɗan Daba, da kuma masu Sha da dallancin kayan Maye a jihar Kano, kuma duk wanda mu ka kama sai mun miƙa shi gurin da ya dace don ɗaukar Mataki, “in ji Inuwa Sharaɗa”.

 

Ya kuma buƙaci iyaye da su ƙara sanya idanu wajen kula akan shige da ficen ƴaƴan su, ta yadda za su zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Continue Reading

Manyan Labarai

Za’a hukunta duk ma’aikacin Shari’ar da aka samu da laifi – Babbar Jojin Kano

Published

on

Babbar jojin Kano mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jaddada cewar kwamitin ladabtarwa na hukumar Shari’a a jihar, zai hukunta duk wani ma’aikaci a tsagin Shari’a matuƙar aka same shi da laifin cin-hanci da rashawa.

Mai Shari’a Dije Aboki ta bayyana hakan ne a yayin taron ƙarawa juna sani wanda hukumar shari’ar ta gudanar ranar Talata, a ɗakin taro na Murtala Muhammad Library da ke Kano.

Taron an shirya shi ne don tunasar da sabbin ma’aikatan Shari’a, akan nauyin da ya hau kan su don mayar da hankali sosai akan batun gujewa cin-hanci da rashawa.

Babbar mai Shari’ar Dije Abdu Aboki, ta bayyana cewar akwai takaddu masu ɗauke da lambobin wayarta da aka liƙe a bangon kotuna, kuma duk wanda aka yi wa ba dai-dai ba zai iya sanar da ita ta kan lambobin kuma za a dauki mataki akan duk ma’aikacin da aka samu da laifi.

Wakilin tashar Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, a yayin taron taron ma’aikatan Shari’a da al’umma da dama ne suka samu damar halarta.

Continue Reading

Hangen Dala

Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Trending