Labarai
Kwamishinan Matasa da Wasanni ya rasu a wani hatsari daga Yobe zuwa Kano

Rahotanni sun bayyana cewa, Kwamishinan matasa da wasanni na jihar Yobe, Hon. Goni Bukar ya rasu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a hanyar Damaturu zuwa Kano.
Marigayin wanda aka fi sani da Bugon, kamar yadda wata majiya mai tushe ta bayyana, ya rasu ne a daren ranar Talata a hanyarsa ta zuwa jihar Kano.
Tun da farko dai Marigayi Kwamishinan, ya halarci sallar jana’izar daya daga cikin mukarrabansa da aka yi a Damaturu babban birnin jihar Yobe kafin ya wuce Kano. In ji Daily Post.
Marigayi Goni Bukar ya kasance tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar Bursari/Geidam/Yunusari a jihar Yobe.
An shirya gudanar da sallar jana’izar kwamishinan wasanni da ya rasu ranar Laraba da misalin karfe 11:30 na safe a masallacin Yobe na Islamic Center dake Damaturu.
Sakon karshe na Bugon akan matsayin sa na WhatsApp da karfe 11:03 na safe, da ya wallafa a Talata:
“Wannan rayuwa da duk abin da ke cikinta, na ɗan lokaci ne”.
Labarai
Rahoto: Mu nisanci abinda Allah Ya hana domin samun saukin rayuwa – Limamin Tukuntawa

Limamin masallacin juma’a na Masjidul Kuba da ke unguwar Tukuntawa a jihar Kano, Malam Ahmad Ali, ya ce, al’umma su duba tsakanin su da Allah tare da nisantar abinda ya hana, domin saukin tsadar rayuwa.
Malam Ahmad Ali, ya bayyana hakan ne, yayin da yake yiwa wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki, Karin bayani dangane da abinda hudubar da ya gabatar ta kunsa.
Akwai cikakken bayanin hudubar a muryar da ke kasa.
Labarai
Rahoto: Rubutu na da muhimmanci a mu’amalar bashi – Limamin Bompai

Limamin masallacin juma’a na Shelkwatar rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ke unguwar Bompai, SP Abdulkadir Haruna, ya ce, akwai bukatar mu rinka gudanar da mu’amalar bashi yadda addinin musulunci.
SP Abdulkadir Haruna, yana bayyana hakan, a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Abba Isah Muhammad, bayar idar da Sallar Juma’a.
Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.
Labarai
Rahoto: Matashi ya yi yunkurin cinye tabar Wiwin da aka kama shi da ita a hanyar kotu

Ana zargin wani matashi ya yi yunkurin hadiye tabar Wiwi da miyagun kwayoyi da aka kama shi da ita a hanyar kotu.
Tunda fari jami’an tsaron, sun kama matasahin da zargin samun sa da kayan maye, inda yake boye da wasu basu sani ba, kafin kuma a kai shi kotu, ya ciro su yana yunkurin hadiye wa.
Wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki yana da cikakken rahoton.
-
Nishadi3 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai2 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi3 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai2 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Lafiya2 months ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi3 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano