Connect with us

Lafiya

A na zargin matashi da kashe kishiyar mahaifiyarsa tare da karya mahaifinsa

Published

on

Wani matashi mai suna Najeeb Shehu Umar, mai shekaru 24, dalibi mai matakin aji na 300 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma a na zarginsa da kashe kishiyar mahaifiyarsa har lahira a gidansu da ke Ambassadors Quarters, Jihar Katsina.

Rahotanni sun ce Najeeb ya kuma karya kafar mahaifinsa da hannu a lokacin da ya yi kokarin shiga lamarin, wanda ya jefa mazauna unguwar cikin rudani.

Mahaifinsa, Shehu Umar Balele, wanda shi ne mai kula da ma’aikatar ilimi ta Katsina, an ce yana karbar kulawar likitoci a sashin kula da kashi na asibitin koyarwa na Katsina, kamar yadda wata majiya mai tushe ta bayyana wa Daily Post.

An rawaito cewa Najeeb a lokuta da dama ya nuna rashin jin dadinsa ga Hajiya Hasiya Galadima mai shekaru 65 da haihuwa tsohuwat ma’aikaciyar gwamnatin jihar Katsina.

An ce Najeeb, wanda ya taba yin ta’ammali da miyagun kwayoyi, a lokuta da dama ya sha yin barazanar kashe kishiyar mahaifiyarsa, bisa zargin cewa ita ce ke da alhakin raba shi mahaifinsa da mahaifiyarsa.

Babban yaron gidan, Mustapha Shehu Umar wanda shi ma yana zaune a gidan tare da matarsa ​​da ‘ya’yansa, yayin da yake tabbatar da rahoton ga DAILY POST, ya kuma bayyana cewa, dan uwansa, Najeeb ya yi barazanar kashe mahaifiyarsu a lokuta da dama, amma mahaifinsu ya hana su daukar mataki a kansa domin yana son yayi karatu.

Sai dai kuma a irin wannan lokacin, sai da suka kai rahoton barazanar ga ‘yan sanda, amma ba a dauki wani mataki na zahiri a kansa ba.

Da yake ba da labarin abin da ya faru, Mustapha ya ce, dan uwansa wanda ya ke da shaye-shaye iri-iri, ya kai wa mahaifiyarsu hari a dakinta a lokacin da danta tilo ya zo gidan dangin.

“Najeeb ne ya shiga falon uwar gidan mu rike da makami ya kulle kofar shiga. Ya tuna mata alkawarin da ya yi zai kashe ta. Sannan ya buge ta a kai da gwaggo har sau biyu sannan ta fadi.

“Yar uwata da ke tare da mahaifiyarmu a zaune, ta ruga ta rike shi. Suna ta faman tureshi. Sannan ta ruga ta bude kofar shiga ta fita da gudu. Yana cikin kiran agaji ya tashi ya bi bayanta, amma da sauri mahaifinmu ya sa baki da gudu daga dakinsa ya kasa zuwa wajenta. Duk da haka, ya sa wa mahaifinmu duka, ya karye masa ƙafa don ƙoƙarin hana shi.

 

Lafiya

Ku rinƙa ziyartar Asibiti ana muku gwaje-gwajen fitsari da Jini domin sanin halin da ƙodar ku take ciki – Likita

Published

on

An shawarci al’umma da su rinƙa ziyartar Asibiti akai akai wajen duba lafiyar su, ta hanyar yin gwaje-gwajen fitsari da jini domin sanin halin da kodar su ke ciki.

Dakta Muhajid Sunusi Rabi’u ne ya bayyyana hakan yayin ganawarsa da Dala FM, lokacin da suke aikin gwaje-gwajen fitsari da jini, kyauta a ɗaya daga cikin makarantu masu zaman kan su a nan Kano.

Dakta Mujaheed ya kuma ce sun gudanar da aikin ne a wani ɓangare na bikin ranar ƙoda ta Duniya, wadda aka ware duk ranar Alhamis ta mako na biyu na kowanne watan Maris domin gudanar da bikin ranar.

Continue Reading

Lafiya

Za’a yiwa kusan yara miliyan 3 rigakafin cutar shan Inna a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano tace kusan Yara miliyan 3 za’ayiwa rigakafin cutar shan inna a kananan hukumomin jihar nan 44, duba da samun ɓurɓushinta da kaso 65, a jihar ta Kano.

Kwamishinan lafiya na jihar Kano Dakta Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da rigakafin cutar shan innar a yau Alhamis, wanda za’a kwashe kwanaki 4 ana gudanarwa a Kano.

Dakta Abubakar Labaran ya ce duba da shigowar zafin akwai buƙatar al’umma su kula da alamomin cutar sankarau, duk da gwamnati ta yi shirin bayar da agajin gaggawa, kamar yadda tashar Dala FM Kano ta rawaito.

Ma’aikatar lafiyar ta jihar Kano dai ta ce za’a ci gaba da gudanar da sauran rigafin, domin bai wa yaran jihar Kano kariya daga cututtuka masu yaɗuwa.

Continue Reading

Lafiya

Dokar tilasta gwajin lafiya kafin aure ta tsallake karatu na biyu a majalisar dokokin Kano

Published

on

Rahotanni na bayyana cewar majalisar dokokin jihar Kano, ta yi karatu na biyu a kan kudirin dokar tilasta wa masu niyyar yin aure yin gwajin cutar kanjamau, da na cutar hanta da kuma duba kwayoyin jini wato Sikila, gabanin daura aure.

Ɗan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Takai, Hon.Musa Ali Kachako, shin wanda ya kawo kudirin dokar, ya bayyana cewa, jihar Kano na fama da matsalolin lafiya daban-daban da suka hada da cutar kanjamau saboda mutane kan yi aure ba tare da an duba lafiyarsu ba, hakan ne ma ya sa ya kai ƙudirin.

Kachako, ya ce, ƙudirin dokar idan har aka amince da shi, zai ceci rayuka da dama tare da dakile yaɗuwar cututtuka masu barazana ga rayuwar al’umma, kamar yadda jaridar Kadaura24 ta rawaito.

Da yake nuna goyon bayansa kan ƙudirin Ɗan majalisa Hon. Aminu Sa’ad, mamba mai wakiltar mazabar Ungogo, ya ce, jihohin Jigawa, Katsina da Kaduna sun zartar da irin wannan kudiri domin magance kalubalen kiwon lafiya da suke fuskanta.

Ya ce tilas ne Kano da ke da yawan al’umma a kasar nan ta zartar da kudirin dokar, domin kare lafiyar ‘yan jiharta ta hanyar samar da gwaje-gwaje kafin aure domin dakile yaduwar cututtuka, kamar cutar hanta, da sauran cututtuka.

Continue Reading

Trending