Connect with us

Labarai

Ranar Bata ta Duniya: Sama da mutane dubu 25 sun bata a Najeriya

Published

on

Kungiyar ba da agaji ta kasa da kasa Red Cross, ta ce alkaluman baya-bayan nan na mutanen da suka bace a fadin Afirka sun kai 64,000, inda Najeriya ta samu sama da mutane 25,000 da suka bace.

Mista Yann Bonzon, shugaban wakilai na al’umma a Najeriya ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, domin tunawa da ranar ‘yan kasa da kasa da ake gudanarwa a kowace ranar 30 ga watan Agusta.

Sanarwar ta samu sa hannun Ms Akpa Esther, jami’ar sadarwa, kuma manazarcin al’umma a Abuja.

Bonzon ya ce, daga cikin sama da 25,000 da aka ce sun bace a Najeriya, sama da 14,000 yara ne.

A cewarsa, ana fama da rigingimu sama da 35 a kasashen Afirka.

Ya ce, dubunnan mutane da suka hada da yara kanana ke keta iyaka da hamadar Sahara da kuma tekun Mediterrenean, domin neman tsira da rayuwa mai inganci a kowace shekara.

Bonzon ya ce irin wannan yakan haifar da babban hadari, gami da hadarin bacewa.

Ya ce, bayanan da aka samu na mutanen da suka bace na karuwa yayin da al’umma suka yi gargadin cewa ainihin alkaluman sun fi haka.

“Abin baƙin ciki, kusan yara 14,000 da aka yi wa rajista ba su cika cikakkiyar wannan al’amari na jin kai da ake watsi da su ba.

“Babu shakka akwai karin yaran da ba a san makomarsu ba,” in ji Bonzon.

Ya ce a lokacin da ake gudun hijira, yara suna fuskantar kasada kamar cin zarafi, tashin hankali, damuwa da kuma bacewar wasu da yawa kuma sun kare su kadai, ba tare da labarin inda iyalansu suke ba.

A cewarsa, al’umma na da fiye da 5,200 da aka rubuta na yara marasa rakiya a Afirka.

Ya kuma ce a shekarar 2022 daga watan Janairu zuwa Yuni, al’umma tare da kungiyar agaji ta Red Cross Society (NRCS), sun taimaka wajen musayar sakonnin Red Cross 1,250 masu dauke da labaran iyali.

Youssef ya ce, al’umma sun hada yara 31 da suka rabu da kananan yara marasa rakiya tare da iyalansu, yayin da aka aika wa iyalai 440 ta wayar tarho don ci gaba da huldar iyali.

“Bugu da kari, iyalan mutane 377 sun samu bayanai game da inda ‘yan uwansu suke ko makomarsu.

“Yayin da iyalai 146 na mutanen da suka bace sun sami tallafin zamantakewa, tattalin arziki, shari’a da gudanarwa ta hanyar Shirin Bayar da Iyalan Bacewar,” in ji shi.  a cewar (NAN).

Labarai

Abin takaici ne yadda ake fuskantar ƙarancin ruwan Sha a sassan jahar mu – Gwamnan Kano.

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya nuna rashin jin daɗin sa bisa yadda ake samun ƙarancin Ruwan Sha, a wasu daga cikin sassa jihar Kano.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga manema labarai, a lokacin a ya kai ziyarar gani da ido, matatar Ruwa da ke Tamburawa a yammacin yau Juma’a, a ƙokarin sa na na gyara ɓangaren ruwan a cikin garin Kano.

Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma sha alwashin tabbatar wa al’umma cewar, gwamnatin sa za ta yi aiki ba dare ba rana domin tabbatar da isasshen ruwan Sha ga al’ummar jihar Kano.

Gwamnan ya ƙara da ce a lokacin da suka zo ba sufi mako biyu ba suka samar da ingantaccen Ruwan sha, wanda ya rinƙa shiga cikin lunguna da Sako na sassan jihar.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da sayar da Burtalai a wasu garuruwan ta

Published

on

Biyo bayan kokawar da wasu Fulani Makiyaya suka yi kan yadda wasu suka gididdiba burtalai yayin da aka siyarwa Manoma, a garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, yanzu haka ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da taɓawa, ko kuma sayar da dukkanin Burtalan kiwon shanun ba tare da ɓata lokaci ba.

Shugaban riƙon ƙaramar hukumar ta Tofa Abubakar Sulaiman Mai Rogo, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a ranar Alhamis.

Mai Rogo, ya kuma ce ƙaramar hukumar ba ta da hannu a kan taɓa dukkan guraren, a dan haka sun dakatar da dukkanin yunƙurin taɓa Burtalan har sai shugabanni na kwamitin ƙasa sun kammala bincike wanda yanzu haka ake ci gaba da yi.

Da yake nuna jin daɗin sa kan matakin dakatarwar, amadadin Fulanin garuruwan, shugaban ƙingiyar Funali Makiyaya ta Gan Allah, Ahmad Shehu Gajida, yabawa gwamnatin jihar Kano, da kuma ƙaramar hukumar ta Tofa ya yi, bisa karɓar koken su da suka akai.

A baya-bayan nan ne dai a zantawar Dala FM Kano, da wasu Funalani Makiyaya mazauna garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, suka koka kan yadda aka gididdiba burtalan a yankunan nasu aka siyarwa manema, lamarin da suka ce ka iya sawa su rasa guraren da za suyi kiwon shanun su wanda hakan babbar barazana ce a gare su.

Continue Reading

Labarai

Ku guji zubar da Shara barkatai a muhallan ku – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta gargadi al’umma da su kaucewa zubar da shara a wuraren da ba’a tanade su ba, domin kaucewa yawaitar samun cutuka a tsakanin al’umma, duba da yadda ake ci gaba da tunkarar lokacin Damuna.

Shugaban hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar Kano Ambasada Ahmadu Haruna Zago, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake sanya ido kan aikin kwashe sharar da ke unguwar Zango hauran gadagi bayan Festival.

Ya ce duba da yadda Damuna ke ci gaba da tunkarowa, akwai bukatar al’umma su fahimci cewa zubar da shara barkatai ka iya haifar da cututtuka daban-daban ga iyalan su, musamman ma kasancewar sharar da ke unguwar ta Zango bayan Festival, tana tsakiyar gidajen al’umma ne da kasuwa da kuma makaranta.

Nazifi Mohammed Usman mai Duniya, da Mohammed Ibrahim wato Halifa mai Gas mazauna unguwar ta Zango ne, sun ce tarin sharar a cikin unguwar su babban ƙalubale ne a gare su, domin kuwa taruwar da tayi har ta kan shiga cikin makarantar yankin su.

Shugaban hukumar kwashe sharar Ahmadu Zago, ya kuma sha alwashin yin duk mai yiwuwa wajen tsafta ce birnin Kano, wajen kwashe shara daga kowane yankin, domin gudun faruwar ambaliyar ruwa sanadin sharar da ka toshe magunan ruwa a jihar Kano.

Continue Reading

Trending