Connect with us

Labarai

Labarai a takaice na yau Talata 30 04 2019

Published

on

5:54 Daliban Jamiar Yusuf Maitama Sule dake nan Kano tare da hadin gwiwar sauran daliban Jami’oi daban daban dake sassa daban-daban na fadin kasar nan tare da hadin kan wasu ‘yan kungiyoyi suka gudanar da wata Zanga-zangar lumana a cikin akwaryar birnin Kano.

Zanga Zangar dai ta samo asali ne bisa zargin wata daliba mai suna Zainab Habibu Aliyu ‘yar asalin jihar Kano da Kasar Saudiyya ta kama ta da kwaya a cikin Jakarta, zanga-zangar sun yi ta ne har zuwa gidan Gwamnatin Jihar Kano domin kai koken su Inda suka sami tarba daga Sakataren Gwanatin Jihar Kano Alhaji Usman Alhaji a madadin Gwamnan Kano Dr.Abdullahi Umar Ganduje daga nan su ka wuce zuwa ofishin jakadancin kasar Saudiyya dake jihar Kano.

A wani cigaban kuma tuni kasar Saudiyya ta saki dalibar Zainab Habiba Aliyu aka kuma mika ta zuwa ofishin jakadancin Nijeriya dake kasar Saudiyya bayan da gwamnatin tarayya ta shiga cikin lamarin inda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci shugaban alkalin alkalai Tanko Muhammad da ya hanzarta shiga cikin lamarin.

Kungiyar likitocin dabbobi ta kasa reshen jihar Kano, ta ce ana iya daukar cutar dabbobin gida har idan suna dauke da wata cuta musamman ma mai saurin yaduwa.

Mataimakin shugaban kungiyar, Dr Aminu Bello Hanga ne ya tabbatar da hakan yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala, ya na mai cewa ”kamata ya yi mutane da su rinka taka tsantsan da dukannin nau’ikan dabbobin da su ke mu’amala dasu musamman ma a lokacin da suka ga wani sauyin yanayi ga dabbobin su”.

Tsohon shugaban makarantar Kwalejin Rumfa dake nan Kano, Malam Tijjani Muhammad Adam, ya yi kira ga tsofaffin dalibai, da su ci gaba da hada kai tare da samarwa makarantun da suka kammala hanyoyin ci gaba.

Malam Tijjani Muhammad Adam, ya yi wannan kiran ne yayin taron tsofaffin daliban makarantar Kwalejin Rumfa aji na shekarar 1998, yayin taron an karrama tsofaffin ‘ya’yan kungiyar wanda suka hada da Dr. Ashir T. Inuwa na sashin koyar da aikin jarida a jami’ar Bayero da ya kammala digirinsa na uku, da kuma Dr. Musbahu Haruna Ahmad, wanda shima ya zama kwararre a bangaren kwakwalwa da laka a Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano.

Mataimakin babban Sufetan ‘yansanda na kasa mai kula da shiyya ta daya, AIG Danbature, ya bude dakin taro na rundunar ‘yansanda ta jihar Kano wanda kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Muhammad Wakili ya sabunta dakin taro a shalkwatar rundunar dake unguwar Bompai.

Taron wanda ya sami halartar manyan jami’an ‘yansanda da kanana da sauran al’ummar gari, inda aka sanyawa dakin taron suna IGP Muhammad Abubakar Adamu, wannan dai na daya daga cikin ayukan da CP Muhammad Wakili yake gudanarwa a jihar Kano bawai iya akan kwaya ya tsaya ba.

Mai Magana da yawun ma’aikatan gidajen yari na jihar Kano, DSP Musbahu Lawan Kofar Nassarawa, yace sashi na dari uku da casa’in da tara na kundin tafikar da tsarin aikin ma’aikatan gidan yari ya baiwa kowane dan kasa damar kai ziyara tare da bada gudunmawa ga dauraru.

DSP Musbahu, ya ce ”a don haka kowa na da damar kai gudunmawarsa ga daurarru tare da kai masu ziyara a fadin kasar nan”.

Limamin massalacin juma’a na Khulafa’urrashidin dake unguwa uku ‘yan awaki, Malam Muhammad Sani Umar Arqam, ya gargadi ‘yan kasuwa da su rinka sassauta farashi don saukakawa al’umma musamman ma a watan Ramadan mai karatowa nan da wasu ‘yan kwanaki.

Ta cikin shirin shari’a a aikace na nan gidan rediyon Dala, a nasa bangaren Malam Yusuf Abdulrahman Yusuf Uba Mandawari wanda ya kasance a cikin shirin, ya bayyana cewa ”matsalar tsaro da ake fama da ita, na da nasaba da talaucin da mutane suka tsinci kan su a ciki”.

Wani kwarraren likita dake aiki a asibitin koyarwa na Aminu Kano, Dr Ibrahim Danjummai, ya shawarci masu dauke da cutar ciwon sukari dasu kaucewa cin abubuwan da za su rinka tayar da masu da cutar su musamman ma cin kitse.

A zantawarsa da gidan rediyon Dala, Dr Danjummai, ya kuma ce ”wadanda basu da wannan cuta sai sun kasance masu motsa jiki akai-akai don gudun kamuwa da cutar ciwon suga”.

 

Labarai

Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.

Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Continue Reading

Labarai

Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.

Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.

“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.

Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.

Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Continue Reading

Labarai

Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Published

on

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.

Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.

Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.

Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

Continue Reading

Trending