Wani daya tsayawa Wanda ake zargi da damfara, ya Kare a kurkuku.

Domin jin cikakken rahoton saurari shirin Baba suda na yau Laraba 01-05-2019. da karfe 10:30 Na dare a tashar DALA FM 88.5


Manta Sabo
Zargin ɓata suna: Kotu ta bada Belin Ƴar TikTok Alpha Chales Borno

Kotun Majistret mai lamba 17 karkashin jagoranci mai Shari’a Huda Haruna Abdu, ta bayar da belin matashiyar yar Tiktok din nan Alpha Charles, wadda Ƴan Sanda suka gurfanar a gaban bisa zargin ta da laifin ɓata suna.
Ƙunshin zargin ya bayyana cewar Alpha Charles, ta ɓata sunan Sadiya Haruna ta dandalin sada zumunta.
Yayin da aka karanta mata tuhumar ta musanta, kuma lauyoyin da suke kare ta sun roki beli, Inda kotun ta sanya ta a hannun beli a bisa sharadin mutum biyu da za su tsaya mata,
Kazalika, sharuɗan Belin sun bayyana cewa, dole ne masu tsayawar na ɗaya ya zama ɗan uwanta na jini, ɗayan kuma ma’aikacin gwamnati mai mataki na 16, idan ta tsere masu karbar belin zasu ajiyewa kotun Naira dubu ɗari biyar.
Sai dai lauyan Alpha ya bayyana wa kotun cewar, Sadiya Haruna ta ɗauki hoto da bidoyon Alpha a harabar kotun ta kuma yaɗa a dandalin Facebook, tare da wasu maganganu da suke zargi na batanci ne.
A don haka kotun ta nemi mai ƙara Sadiya Haruna, sai dai an neme ta sama ko ƙasa ba a ganta ba, an kuma umarci lauyanta da ya gabatar da ita.
Wakilin Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, kotun ta sanya ranar 28 ga wannan watan Afrilun da ake ciki na shekarar 2025, don ci gaba da sauraron shari’ar.

Manyan Labarai
Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.
Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.
Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.
A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.
Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Manyan Labarai
Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.
Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.
“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.
Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.
Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.
Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.
Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su