Wani daya tsayawa Wanda ake zargi da damfara, ya Kare a kurkuku.
Domin jin cikakken rahoton saurari shirin Baba suda na yau Laraba 01-05-2019. da karfe 10:30 Na dare a tashar DALA FM 88.5
Manyan Labarai
Ba harkar siyasa ce ta ƙare mini ba nake yin waƙoƙin su Fatima Mai Zogale da A’isha Humaira- Rarara
Fitaccen mawaƙin siyasar nan kuma ɗan masana’antar Kannywood Dauda Adam Kahutu Rarara, ya ce batun da wasu suke yaɗawa cewar ya yiwa Fatima mai Zogale kyautar Mota, lamarin ba gaskiya ba ne.
Dauda Rarara ya bayyana hakan ne ta cikin shirin daga Kannywood na tashar Freedom Radio da ya gudana a daren jiya Juma’a, ya kuma ce duk wanda ya bai wa kyautar Mota, Babur ko Kuɗi, ba shi ne ya ke cewa suyi hoto da mutum ba, “A,a wanda na bai wa ne da kan sa ya ke cewa mu ɗauka”.
Ko da aka yi masa tambaya akan ko yana neman muƙami ne a gwamnatin tarayya, Rarara, ya ce, Ba Muƙami yake nema a siya ba, domin inda ace muƙamin yake nema da tuni ya samu.
Har ila yau, Rarara ya ƙara da cewa ba harkar siyasa ce ta kare masa ba ya ke yin waƙoƙin su Aisha Humaira da Fatima Mai Zogale ba, kamar yadda kafar yaɗa labarai ta Dala FM Kano ta rawaito.
Labarai
Abin takaici ne yadda ake fuskantar ƙarancin ruwan Sha a sassan jahar mu – Gwamnan Kano.
Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya nuna rashin jin daɗin sa bisa yadda ake samun ƙarancin Ruwan Sha, a wasu daga cikin sassa jihar Kano.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga manema labarai, a lokacin a ya kai ziyarar gani da ido, matatar Ruwa da ke Tamburawa a yammacin yau Juma’a, a ƙokarin sa na na gyara ɓangaren ruwan a cikin garin Kano.
Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma sha alwashin tabbatar wa al’umma cewar, gwamnatin sa za ta yi aiki ba dare ba rana domin tabbatar da isasshen ruwan Sha ga al’ummar jihar Kano.
Gwamnan ya ƙara da ce a lokacin da suka zo ba sufi mako biyu ba suka samar da ingantaccen Ruwan sha, wanda ya rinƙa shiga cikin lunguna da Sako na sassan jihar.
Labarai
Ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da sayar da Burtalai a wasu garuruwan ta
Biyo bayan kokawar da wasu Fulani Makiyaya suka yi kan yadda wasu suka gididdiba burtalai yayin da aka siyarwa Manoma, a garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, yanzu haka ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da taɓawa, ko kuma sayar da dukkanin Burtalan kiwon shanun ba tare da ɓata lokaci ba.
Shugaban riƙon ƙaramar hukumar ta Tofa Abubakar Sulaiman Mai Rogo, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a ranar Alhamis.
Mai Rogo, ya kuma ce ƙaramar hukumar ba ta da hannu a kan taɓa dukkan guraren, a dan haka sun dakatar da dukkanin yunƙurin taɓa Burtalan har sai shugabanni na kwamitin ƙasa sun kammala bincike wanda yanzu haka ake ci gaba da yi.
Da yake nuna jin daɗin sa kan matakin dakatarwar, amadadin Fulanin garuruwan, shugaban ƙingiyar Funali Makiyaya ta Gan Allah, Ahmad Shehu Gajida, yabawa gwamnatin jihar Kano, da kuma ƙaramar hukumar ta Tofa ya yi, bisa karɓar koken su da suka akai.
A baya-bayan nan ne dai a zantawar Dala FM Kano, da wasu Funalani Makiyaya mazauna garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, suka koka kan yadda aka gididdiba burtalan a yankunan nasu aka siyarwa manema, lamarin da suka ce ka iya sawa su rasa guraren da za suyi kiwon shanun su wanda hakan babbar barazana ce a gare su.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su