Connect with us

Labarai

Watan Nuwamba za mu fara baiwa ma’aiakata albashin dubu 30 – Zamafara

Published

on

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Mohammed Matawalle, ya baiwa shugabannin kwadago tabbacin cewa, gwamnatin sa za ta aiwatar da mafi karancin albashi na Naira 30,000 a karshen watan Nuwamba, 2022.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da shugabannin kungiyar kwadago ta kasa NLC su ka kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati Gusau, babban birnin jihar.

Gwamna Matawalle ya ce, gwamnatinsa ta na da ra’ayin daukacin ma’aikata a jihar a matsayinta na tsohon ma’aikacin gwamnati, domin haka gwamnatinsa ta yanke shawarar samar da duk wani hakki ga ma’aikata.

“Gwamnatina za ta fara aiwatar da mafi karancin albashi na N30,000 ga daukacin ma’aikatan jihar nan da watan Nuwamba, 2022,” in ji shi.

Matawalle ya ce, za a ci gaba da baiwa ma’aikata da ’yan fansho fifiko daga gwamnatinsa, domin samun biyan bukatunsu na gudanar da ayyuka masu inganci.

Gwamnan ya yi kira ga kungiyoyin kwadago da ke jihar da su taimaka wa gwamnati ta hanyar toshe duk wata badakala da zamba a tsakanin ma’aikatan gwamnati, domin ta samar da duk wani tallafi da jin dadin ma’aikata.

Dangane da biyan kudin giratuti ga ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya, Gwamna Matawalle ya ce gwamnatin jihar za ta aiwatar da cikakken biyan kudaden da zaran an daina cire kudaden jihar daga watan Disamba na wannan shekara.

A cewarsa, gwamnatinsa za ta gina gidan da ya dace da kungiyar kwadago a Gusau, babban birnin jihar domin bunkasa ayyukan kungiyar kwadago ta NLC da kungiyar kwadago da kuma kungiyoyin kwadago a jihar.

Ya sanar da cewa gwamnatin jihar ta kammala shirye-shiryen samar da kayan abinci ga daukacin ma’aikatan jihar a kan lamuni a kan farashi mai ma’ana.

Tun da farko, shugaban kungiyar NLC na jiha, Kwamared Sani Halliru, da takwaransa na kungiyar ‘yan kasuwa TUC, Kwamared Sa’idu Mudi Allahuwa, sun bayyana cewa sun je gidan gwamnati ne domin nuna jin dadinsu ga gwamnan bisa amincewar sa na aiwatar da N30,000. mafi karancin albashi na kasa.

Taron ya samu halartar tsohon Ministan Kudi wanda ya zama shugaban kwamitin aiwatar da mafi karancin albashi na kasa a jihar Zamfara, Ambasada Bashir Yuguda Gusau, sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Kabiru Balarabe Sardauna.

Sauran sun hada da shugaban ma’aikatan gidan gwamnati, Malam Ibrahim Suleiman; Shugaban ma’aikata na jiha, Alhaji Kabiru Muhammad Gayari; Mataimakin shugaban ma’aikatan gidan gwamnati, Comrade Jalaluddeen Maradun; Kwamishinan yada labarai da ayyuka na musamman, Alhaji Ibrahim Dosara; da Alhaji Abdulaziz Ahmed Nahuce.

Shi ma mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin kwadago da siyasa, Kwamared Bello Galadima Durumbu ya halarci taron.

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending