Connect with us

Labarai

Labarai a Takaice na yau Litinin 06 05 2019

Published

on

Kungiyar bunkasa ilimi da cigaban demokradiyya da samar da daidaito a zamantakewa SEDSAC, ta yi kira ga ‘yan kasuwa da su ji tsoron Allah wurin kaucewa Karin farashin kayan abinci a wannan lokaci na watan Azumin Ramadan.

Cikin wata takarda mai kunshe da sa hannun sakataran shirye-shiryen kungiyar, Kwamrade Abubkar MD Mukhtar ya sanyawa hannu, ta bukaci ‘yan kasuwa da su sassautawa al’ummar musulmai wajen ganin sun sami kayan abinci cikin sauki, haka zalika kungiyar ta kuma yi kira ga masu hannu da shunni dasu rinka tallafawa mabuka.

A ranar daya ga watan Ramadan ne Allah madaukakin sarki, ya aiko fiyayen halita a matsayin Annabi, kuma a wannan rana ce Annabi (SAW) ya fara ganin mala’ika Jibril a kogon Hira.

Haka zalika a wannan rana ce ta daya ga watan Ramadan, Annabi ya auri matar sa Zainab Bintu Khuzaima uwar miskinai, kuma wannan rana ce Annabi S.A.W ya fara yin sallar rokon ruwa.

Shugaban makarantar Zinatul Islam wa tahfizil kur’an dake Rafin Malam a karamar hukumar Ungogo, Ahmad Isma’il Ibrahim, ya yi kira ga daliban makarantar da su kiyaye kimar da Allah ya yi masu na hadace al’kurnai da su ka yi.

Ahmad Isma’il Ibrahim, ya yi wannan kiran ne yayin saukar daliban makarantar karo na farko da suka haddace al’kurani har su 14, inda ya kuma yabawa malaman makarantar bisa yadda suka jajirce wajan kula da karatun daliban.

Mataimakin kungiyar taimakon kai da kai wato ZUDA dake yankin unguwar Hausawa ta gidan Zoo, Usaini Haruna Kailu, ya bukaci masu hannu da shuni da ‘yan kasuwa da su rinka tallafawa marasa karfi a unguwannin su, musamman marayu.

Usaini Haruna Kailu, ya yi wannan kiran ne yayin rabon kayan abinci da kungiyar ta raba ga marayun yankin ciki akwai buhun shinkafa 145 da kuma katan din taliya 40.

Labarai

Zamu magance ƙalubalen da ake samu a fannin ilimi mai zurfi – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jahar kano ta sha alwashin mangance dukkanin wani ƙalubale a fannin ilimi mai zurfi a fadin jihar Kano.

Kwamishinan ilimi mai zurfi Dakta Ibrahim Yusif kofar mata, ne ya
bayyana hakan a yayin taron yaye daliban kwalejin ilimi ta Aminu
Kano (AKCOE), da ya gudana a ranar Alhamis.

Y kuma ce yanzu haka tattaunawa tayi nisa a hukumance akan bukatar kwalejin dan ganin ta samu wadataccenf ilin da za ta gina jami’a.

Dakta Ibrahim kofar mata ya bayyana gamsuwa da tsarin da kwalejin take bi wajen gudanar da karatu, inda ya kuma ja hankalin dalibai 40 da suka karbi shaidar kammala karatun NCE,
da su zama ababen koyi.

Da yake nasa jawabin shugaban kwalejin Dr. Ayuba Ahmad Muhammad, ya ce da zarar sun shiga sabon tsari za su fara da daukar dalibai yan asalin jahar Kano mutum dubu daya kyauta, tare da biyawa ‘yan makarantar
kudi sama da Naira miliyan 300 yan asalin jahar kano dan
karfafawa matasa gwiwa.

Wakilinmu Yusif Nadabo Isma’il ya rawaito cewa al’umma da dama ne suka samu damar halartar taron daga guraren daban-daban na jihar Kano, da ma ƙasa baki ɗaya.

Continue Reading

Labarai

Bama jin daɗin yadda wasu iyaye suke hana ƴaƴan su maza auren mu – Budurwa mai larurar Ƙafa

Published

on

Wata matashiyar budurwa mai buƙata ta musamman dake da lalurar Ƙafa Samira Ahmad Tijjani, ta nuna rashin jin daɗin ta, bisa yadda mafi yawan iyaye suke nunawa masu lalurar ƙyama, wajen hana ƴaƴan su auren masu lalurar ƙafar lamarin da yasa al’amarin ke matuƙar ɓata musu rai.

A zantawar wakilinmu na ƴan Zazu Hassan Mamuda Ya’u, da budurwar ta ce, mafi yawancin su mata masu lalurar ƙafar sun ma fi mata masu lafiya iya Girki, da sauran ayyukan yau da kullum.

Ta ci gaba da cewa, “Amma abin takaici sai a rinƙa nuna mana ƙyama, ko kuma wariya musamman ma wajen neman aure, bayan kuma ba mu muka yiwa kan mu halitta ba, “in ji Samira”.

Ta kuma ce abinda wasu daga cikin iyaye suke yi musu kan nuna ƴaƴan su ba za su aure mai lalurar Kafa ba, basa jin daɗin hakan, shi yasa ma ta fito domin ta sanarwa al’umma domin gujewa hakan.

A cewar ta, “Ko nima nayi soyayya mara misaltuwa da samari masu lafiyar Ƙafa, amma mahaifiyar ɗaya daga cikin su ta ce ita ba wai bata sona ba, amma tana jin kunyar ta tuna ni a cikin mutane cewar a zummar matar ɗan ta”.

Daga bisani dai ta yi kira ga al’umma da su dai na nuna ƙyamar ko kuma nuna wariya a gare su, bisa yadda iyayen su suke matuƙar shiga cikin damuwa a duk lokacin da aka nuna musu wariyar.

Continue Reading

Labarai

Bayan ƙaddamar da tallafi: Zamu rinƙa raba tallafin jarin Naira dubu 50,000 ga iyaye Mata duk wata – Gwamnan Kano

Published

on

Gwamnatin jihar kano ta kaddamar da rabon taffin kuɗaɗe ga iyaye mata dake kananan hukumoni 44 su 5,200 a fadin jihar nan, domin su dogara da kan su.

Gwamnan kano Injiniya Abba Kabir Yusif, ne ya jagoranci ƙaddamar da rabon tallafin kudaɗen har Naira 50,000 ga iyaye mata dake kananan hukomini 44 a yau Talata, wanda ya gudana a ɗakin taro na Coronation Hall da ke gidan gwamnatin kano.

Abba Kabir Yusif ya kuma ce hakan na daga cikin alkawarin da suka yiwa matam tun a lokacin yaƙin neman zaben shekarar 2023 da ta gabata, inda ya ce iyaye mata na da bukatar jari domin dogaro da kan su, musamman ma wajen yin sana’o’i irin su Kosai, Awara, Gurasa da Bandasho da dai sauran ƙananan sana’o’i.

Aƙalla dai Mata ɗari-ɗari ne 100, za su amfana daga kananan hukumomi 36 na Karkara, da kuma na cikin birni takwas 8, kuma iyaye mata dari biyu-biyu (200) za su amfana da tallafin duka dai domin su dogaro da kan su.

Wakilinmu Abba Haruna Idris ya rawaito cewa Gwamnan Kano Abba Kabir, ya ƙara da cewa wannan ba shine na karshe ba, za su rinƙa tallafawara duk wata-wata, domin samawa iyaye mata sana’oin dogaro da kai, ta yadda zasu rinƙa haɓɓaka tattalin arzikin jihar kano.

Continue Reading

Trending