Manyan Labarai
Za a yanke hukunci neman tsige Buhari da jam’iyyar HDP ta shigar da kara
Mai shari’a Inyang Edem Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja a ranar Juma’a, ya sanya ranar 30 ga watan Janairun shekara mai zuwa, domin yanke hukunci kan karar da ke neman tsige shugaban kasa, Muhammadu Buhari daga mukaminsa da kuma dakatar da gudanar da zaben shugaban kasa na 2023.
Alkalin kotun ya sanya ranar yanke hukuncin ne biyo bayan amincewa da jawabin karshe da shugaba Buhari, da babban lauyan gwamnatin tarayya, da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da kuma mai shigar da kara, Cif Ambrose Albert Owuru suka yi.
A zaman da aka yi ranar Juma’a, Cif Ambrose Albert Owuru, dan takarar shugaban kasa a zaben 2019 a karkashin jam’iyyar Hope Democratic Party (HDP), ya bukaci babbar kotun tarayya da ta dakatar da INEC daga gudanar da zaben shugaban kasa na 2023.
Ya yi wannan kiran ne bisa hujjar cewa, shi ne ya lashe zaben shugaban kasa a 2019 da kuma cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kwace wa’adin mulkinsa.
Ya roki kotu da ta tsige Buhari ta kuma ayyana shi (Owuru) a matsayin ingantaccen shugaban kasa, sannan kuma a tursasa Buhari ya mayar da duk wasu kudaden da ya karba a matsayin albashi da kudaden alawus-alawus da na tsaro.
Owuru, ya kuma bukaci kotun ta ba da umarnin rantsar da shi na tsawon shekaru hudu bayan tsige Buhari daga mukaminsa.
Babban Lauyan ya bayyana wa kansa da Hope Democratic Party HDP sannan kuma ya ba da hujjar karshe.
Owuru da jam’iyyar HDP, sun kai karar shugaba Buhari da wasu mutane biyu suna neman kotu ta bayar da umarnin bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2019.
Ya kuma yi ikirarin cewa shi ne ya lashe zaben raba gardama da aka gudanar a shekarar 2019 kuma tun a wancan lokacin ne aka nada Buhari.
Manyan Labarai
Za’a ɗauki mataki akan duk wanda yake da hannu Gini ya ruftawa mutane a Kuntau – Ƙaramar hukumar Gwale.
Yayin da wani ginin Bene mai hawa biyu ya danne aƙalla sama da Leburori goma a unguwar Kuntau kusa da KEDCO, a safiyar yau Juma’a, Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Gwale Abubakar Mu’azu Mojo, ya ce za’a ɗauki mataki akan dukkan wanda aka samu da laifi har al’amarin ya faru.
Abubakar Mu’azu Mojo, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da manema labarai, yayin da ya ziyarci gurin da lamarin ya faru lokacin da ake ci gaba da aikin ceto mutanen.
Mojo, ya kuma ce babu makawa za’a ɗauki matakin doka akan duk wanda aka samu da hannu akan faruwar lamarin, kama daga ɗan kwangilar da aka bai wa aikin ginin, zuwa kuma mamallakin gidan.
Rahotanni sun bayyana cewa zuwa tsakar ranar yau aƙalla mutane bakwa aka ciro daga ƙasan ginin shida daga cikin su basa iya motsa jikin su, yayin da hukumomi suka ci gaba da gudanar da aikin ceto sauran mutanen da ginin ya danne.
Manyan Labarai
Sulhu da ƴan Bindiga ba zai haifar da Ɗa mai ido ba – Human Rights
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta ƙasa da ƙasa wato International Human Rights Commission, ta ce sulhu da ƴan bindiga ba zai haifar da Ɗa mai ido ba a ƙasar nan.
Babban daraktan ƙungiyar Kyaftin Abdullahi Bakoji Adamu mai ritaya, shi ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano.
Ya ce kasancewar ƴan bindigar basu da wata manufa bai kamata ayi sulhu da su ba, mai-makon hakan yafi dacewa a rinƙa ɗaukar tsauttsauran mataki akan su duba da yadda suke cutar da al’umma.
Ya kuma ce batun da mai bai wa shugaban ƙasa akan sha’anin tsaro Malam Nuhu Ribaɗo, ya yi a baya baya nan, kam cewar an fara samun fashimtar juna da wasu daga cikin ƴan Bindigar da suka addabi mutane a sassan ƙasar nan, a wani ɓangare ma kama da yin sulhu da su, ya faɗi hakan ne kawai amma hakan ba zai haifar da Ɗa mai ido ba.
Manyan Labarai
Gwamnatin Kano ta kulle wata makaranta mai zaman kan ta a jihar
Gwamnatin jihar Kano ta rufe wata makaranta mai suna Golden Crown International School a jihar, da ke yankin Sabon gari, bisa zargin an fake da sunan makarantar ana haɗa magani mara inganci mai-makon koyar da karatu a ciki.
Shugaban kwamitin yaki da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya na jihar Kano General Gambo Mai Aduwa Mai ritaya, ne ya bayyana hakan, a lokacin da Kwamitin ya kai wani sumame da karfe uku da rabi na daren jiya Talata.
Rahotanni sun bayyana cewa makarantar tana kan titin Zungero da ke cikin ƙaramar hukumar Fagge a jihar Kano, wanda bayan samun bayanan sirri aka ɗauki matakin kulle ta.
Mai Aduwa, ya ƙara da cewar tsarin gurin ta waje ya nuna makaranta ce amma kuma sai ake sarrafa magani da ake zargin ingancin sa da bai kai yadda ya kamata ba, tare da ajiye Allurai da kayan haɗa magani cikin ajujuwan mai-makon ɗalibai.
“Za mu faɗaɗa bincike akan al’amarin dan sanin matakin da za mu ɗauka na gaba, “in ji shi”.
Suma masu gadin gurin da muka zanta da su sun bayana cewar, aikin gadi kawai suke yi amma basu da masaniyar abubuwan dake gudana a cikin makarantar, da ake zargin ana sarrafa magani mara ingani da ajiye shi a muhalin da ake zargin bai yi dai-dai da tsarin doka ba.
Wakilinmu Abba Isah Muhammad ya rawaito cewa shugaban kwamitin ya ce, zai ci gaba da bibiyar guraren dake yin abubuwan da za su kawo koma baya ga harkokin lafiya, da ci gaban jihar Kano, musmman wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su