Manyan Labarai
Za a yanke hukunci neman tsige Buhari da jam’iyyar HDP ta shigar da kara

Mai shari’a Inyang Edem Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja a ranar Juma’a, ya sanya ranar 30 ga watan Janairun shekara mai zuwa, domin yanke hukunci kan karar da ke neman tsige shugaban kasa, Muhammadu Buhari daga mukaminsa da kuma dakatar da gudanar da zaben shugaban kasa na 2023.
Alkalin kotun ya sanya ranar yanke hukuncin ne biyo bayan amincewa da jawabin karshe da shugaba Buhari, da babban lauyan gwamnatin tarayya, da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da kuma mai shigar da kara, Cif Ambrose Albert Owuru suka yi.
A zaman da aka yi ranar Juma’a, Cif Ambrose Albert Owuru, dan takarar shugaban kasa a zaben 2019 a karkashin jam’iyyar Hope Democratic Party (HDP), ya bukaci babbar kotun tarayya da ta dakatar da INEC daga gudanar da zaben shugaban kasa na 2023.
Ya yi wannan kiran ne bisa hujjar cewa, shi ne ya lashe zaben shugaban kasa a 2019 da kuma cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kwace wa’adin mulkinsa.
Ya roki kotu da ta tsige Buhari ta kuma ayyana shi (Owuru) a matsayin ingantaccen shugaban kasa, sannan kuma a tursasa Buhari ya mayar da duk wasu kudaden da ya karba a matsayin albashi da kudaden alawus-alawus da na tsaro.
Owuru, ya kuma bukaci kotun ta ba da umarnin rantsar da shi na tsawon shekaru hudu bayan tsige Buhari daga mukaminsa.
Babban Lauyan ya bayyana wa kansa da Hope Democratic Party HDP sannan kuma ya ba da hujjar karshe.
Owuru da jam’iyyar HDP, sun kai karar shugaba Buhari da wasu mutane biyu suna neman kotu ta bayar da umarnin bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2019.
Ya kuma yi ikirarin cewa shi ne ya lashe zaben raba gardama da aka gudanar a shekarar 2019 kuma tun a wancan lokacin ne aka nada Buhari.

Manyan Labarai
Shekaru 63 na Nigeria:- Jawabin Gwamnan Kano

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya buƙaci shugabanni da saura al’umma da suyi koyi da tsaffin shugabannin da suka gabata wajen kawowa ƙasar nan ci gaba da zaman lafiya musamman a irin wannan lokaci.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yau yayin da yake jawabi kan cikar ƙasar nan shekara 63 da samun kyancin kai daga hannun turawan mulkin mallaka.
Gwamna Abba ya kuma ce la’akari da yadda ake tunawa da tsaffin shugabanni wajen ciyar da ƙasar nan gaba ya kamata su shugabannin yanzu suyi koyi da su.
Ka zalika ya ƙara da cewa ya kamata shugaban ni su tabbata sun yiwa al’umma abin da suke buƙata domin tabbatar adalci.
Gwamnatin tace zata ci gaba da gudanar da aikin ta kamar yadda ta tsara domin ciyar da Kano gaba.

Hangen Dala
Hukuncin Kaduna :- PDP za ta daukaka kara

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kaduna ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ta tabbatar da zaben Gwamna Uba Sani na jam’iyyar APC, inda ta ce za ta garzaya kotun daukaka kara.
Alberah Catoh, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar PDP ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a a Kaduna.
Catoh ya ce, wani nazari da lauyan PDP ya yi ya nuna cewa hukuncin bai cika wasu ka’idoji na tabbatar adalci ba.
Martanin ya zo ne sa’o’i bayan kotun da ke zamanta a Kaduna ta amince da nasarar zaben Sani.
Ya kara da cewa hukuncin bai dace da wasu dokoki da ka’idojin zabe ba.
Sanarwar ta kara da cewa, “Saboda haka jam’iyyar ta umurci lauyoyinta da su daukaka kara kan hukuncin da aka yanke a kotun daukaka kara da ke Abuja a cikin wa’adin da doka ta kayyade.”
Catoh ya kuma bukaci magoya bayan jam’iyyar PDP a fadin jihar da su kwantar da hankalinsu tare da nuna kwarin gwiwarsu kan lamarin.

Hangen Dala
Abba ya biyawa Daliban Kano kudin makaranta

Abba Kabir ya biya kuɗin makarantar ɗaliban Jami’ar Bayero
Gwamnatin jihar Kano ta ce, ta biya kuɗin makarantar ɗaliban Jami’ar Bayero, waɗanda ba su samu damar biya ba, kimanin Naira Miliyan ɗari bakwai.
Sakataren hukumar bayar da tallafin ilimi ta jihar Kano, Hon. Kabir Getso Haruna ne, ya bayyana hakan a ranar Talata.
Yana mai cewa, “Yanzu haka Gwamnatin Kano, ta biya wa ɗalibai ƴan asalin jihar, dubu bakwai kuɗin makarantar”.
Ya kuma ce, “Daga yau Talata, dukkan ɗaliban, su tafi Jami’ar Bayero, tsangayoyin su, domin ƙarasa rijista na shekarar 2023, su ci gaba da karatu”. Inji Hon. Kabir Getso.

-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya1 year ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano